1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Azal Part 3

Azal Part 3

By Abdul Mk
Add Comment
Wednesday, 16 March 2016

Dan Hajiya ya nufi gadon da Hajiyansa ta ke da sauri ya kama hannunta, sa’an nan ya fashe da kuka. Lokacin da a ka kira shi a ka sanar masa cewa lallai-lallai ya zo tana nemansa bai san cewa mutuwa za ta yi ba,
Likita ya bi gawar Hajiya da fuskar tausayawa sa’an nan ya dawo da kallonsa kan Banzan d’an ta
”Saboda tana son sanar da kai wani muhimmin al’amari ta so ta gan ka kafin mutuwarta, ashe ba ku da sauran rabon ganawa a duniya.”
Ya juya ya fita a dakin, ya bar Dan Hajiya da nadama da tunanin nasihar da ta yi ta masa a baya, ya tuno da wani lokaci day a bar ta ya tafi gidan Yarinyarsa Linda bai dawo ba sai bayan kwana biyu, kwana biyun da Hajiyansa ba ta runtse idonta ba da nufin barci ko gyangyadi. Ya shigo cikin falon ba tare da ya yi sallama ba, Hajiya ta bi shi da kallo cike da fushi ba tare da ya lura da ita ba, lokacin da ya lura da ita sai karasa gurinta da sauri ya durkusa.
”Hajiya ina kwana? Ai ban gan ki ba saboda tsabar barci da ya rufe mini idanu, hurhudu nake ganinki Hajiyata.”
Ta yi murmushi, amma na karfin hali ne kawai.
”Ai ba abun mamaki ba ne in ka ganni tara-tara ma.
”
Ya sunkui da kansa kasa
“Hajiya a masallaci fa nayi kwanaki biyun nan, kai Allah ya kara mana son Annabi.”
Ta yi busasshen murmushi.
”Dan nan Kaza tana take ‘ya’yanta ne ba don ba ta son su ba, saboda haka duk abun da zan fada maka gaskiya na ke fada maka, gyara kayanka ne.”
.
“Hajiya wallahi ina jin wadannan wa’azaozin naki, amma matsalar da a ke samu ita ce daga na fita a nan sai na neme su na rasa.”
Ta kuma yin murmushi
”Ni dai abun da nake so da kai shine ka bar duk wadannan ayyukan asshan da kake, shin za ka so a na aikata tsinanniyar rayuwa da ‘yar uwarka kamar yadda kai kake da na wasu, kuma ko ba don haka ba ma, ka duba fa kai ne babba a cikin ‘ya’yana, kai nake kallo, shin ba ka tunanin damuwar da nake ciki a duk lokacin da a ka zo mini da labarin ba dadi game da kai?”
.
“Tunanin da na kasa yi kenan har yau, mai yasa bana tunanin damuwarki Hajiya ta?”
Ya fara mikewa da niyyar barin wurin, ta bi shi da kallo
”Allah ya shirye ka.”
”Ameen sama-sama, Hajiyata.”
.
Damuwar da bai yi tunaninta ba har zuwa fitar numfashinta na karshe! Duk duniya ita kadai ce ta damu das hi, ‘yan uwa da sauran dangi sun yi banza da shi saboda bakin halinsa, yanzu rayuwa ta zame masa ba shi da kowa kenan!
Ya dawo a tunaninsa da ganin ‘yan sanda biyu Mudi da Tanko sun cuso masa bindiga a ka , daya yana kokarin sa hannunsa a cikin ankwa.
“You are under arrest!”
Ya juyo ya kalle su da fuskar kuka.
”Ranka ya dade da alama dimuwa kuka yi, ku bar ni na ji da abun da yake damuna.”
Tanko ya yi murmushi
”A na zarginka da laifin kisan kai, barinka a kowanne irin yanayi shine babbar katobarar aikinmu na shekara goma sha tara.”
Dan Hajiya ya zaburaa
”Ranka ya dade ni ko kiyashi ban taba kashewa ba.”
Mudi ya mayar masa da cewa
”Saboda ba ka da matsala da shi ne, kana bata mana lokaci.”
Zai karasa in da yake ya sa masa hand-corp ya ci gaba da cewa
”Mu je ka nuna mana in da ka boye abokiyar aikin naka.”
.
”Ranka ya dade wallahi kaina ya kulle bana gane komai, ku mini hakurin duk wani abu sai bayan na gama yiwa gawar Mahaifiyata gata sa’an nan in yankan naman jikina ma za ku yi a shirye nake.”
Tanko ha Harare shi
“Idan ba ka mata gata ba a halin rayuwa, kila ma bakin cikin halin ka ne yayi sanadiyyar bugawar zuciyarta, wanne gata kuma za ka mata bayan ranta?”
Za su tasa keyarsa a cikin waigen kallon gawar Hajiyarsa, ba kukan kewa da rabuwa da ita kawai yake ba, har da na sabuwar rayuwar da ke shirin kusantarsa, abun bakin cikin shine zai dau tsawon lokaci na rashin haduwa da yarinyarsa Linda!
Shin wa zai warware wannan al’amarin? Wace ce Sadiya, bakar bakuwar da ya marabta, ta gudu ta bar shi da Jidali? A ina zai ganta ya kalli tsabar idonta ya ce da ita “Kin cuce ni. "
Wace ce Sadiya? Bakuwar da Dan Hajiya ya marabta , ita kuma ta gudu ta bar shi da Jidali.
Rayuwarta ta kafin aure sassauka ce, ta bayan aure c eta zo ma ta sabanin zato, ta zo ma ta da rudani da jumurda.
Ranar da take farin ciki, ranar cikar muradinta, Jama’a suka yi tururuwa a kofar gidansu a ka daura aurenta, Sadiya tana farin ciki ta samu Mubarak.
Da daddare a ka kai ta gidan Mijinta, Sadiya tan a farin ciki ga ta a gidan Mubarak da lullubabbiyar fuska tana jiran Abokansa su kawo ma ta shi, Sadiya tana so tag a farin cikin da ya ke cewa zai nuna mata, Sadiya tana ta zumudin zuwan Mubarak.
.
09:37 PM
Ango da Abokansa biyu Sunusi da Musa suka shigo gidan, suna hira da dararraku.
”Ango ka sha kamshi.”
Musa y ace das hi, yayi da Mubarak yake gyara babbar rigarsa yana murmushi
”Kar ka so ka ga yadda nake zumudin zuwan wannan ranar,amma ban san mai ya faru ba daga shigowa ta gidan nan, na nemi walwala ta ba rasa.”
Sunusi ya tabe baki
”Ya kake fadar ka nemi walwalarka ka rasa da fuskar murmushi?”
Suka tsaya suna kallon juna suna murmushi.
”Ka dai san ba zan fada da fuskar kuka ba, koma dai yaya ne abun da nake so na fada muku shine, na tsinci kaina a wani yanayi da bana farin ciki.”
.
SADIYA BED ROOM-
Sadiya a zaune a gefen gado a cikin kayan amarci, fuskarta lullube da mayafinta , Mubarak da Abokansa sua shigo bayan , Kowa ya nemi gurin zama in ban da Mubarak da ya zauna a kusa da ita.
Musa da Sunusi suka kalli juna sa’an nan suka yi murmushi.
“Da alama za mu sha bakar wahala kafin bakin amaryar nan ya sayu. Kila Haka ne ya sa Kawayenta suka gudu suka bar mu daga mu sai ita saboda mu yi ta fama.”
Cewar Sunusi, yayin da Musa ya ce
“Kila dai kai kadai kake ganin wahalar, amma ni bana hango komai sai saukin kan ta, da saukin halinta.”
Mubarak ya kalle ta ya dawo da hankalinsa kan su
ya ce
”Batunka shine gaskiya Musa.”
Sunusi ya tabe baki
“Ni kuma nawa karya ko?”
Suka fashe da dariya gaba daya
”To dai shikenan, shawarar mu gare ku ba ta wuce wacce kuka saba ji ba, ku qi ku qi gani, kuma ku mayar da komai ba komai ba, ku zauna da juna cikin hakuri da girmamawa, wadannan sune gishirin zamantakewa.”
Abokan Mubarak suna ta yi musu nasiha, har zuwa tsawon lokacin da suka mike da shirin tafiya, Sunusi ya ce
”Kai, da alama zumudin ganin amaryar nan ba zai bar ka ka mana rakiya ba.”
Mubarak ya yi murmushi
”Ban da abun ka, ko ba domin rakiya ba, ai zan je na rufe kofar gidana.”
Suka yi sallama da Amarya, Mubarak ya biyo bayansu, Amarya Sadiya tana ta babbaka dariyaa a cikin mayafinta, tana ta ganin kamar rike lokacin a ke a duniyar zumudinta, tana so Mubarak ya yi sauri ya je ya rufe kofa ya dawo gare ta… Sadiya tana ta zumudin ganin farin cikin da ya yi ta ambaton zai ba ta yayin hira da zamantakewar soyayyarsu.
Sai dai abun da Sadiya ba ta sani ba shine Angonta ba zai dawo gare ta ba a wannan lokacin, yana kan hanyar zuwa gidan yarinyarsa Cecelia.

KARFE DAYA NA DARE
DAKIN SADIYA
.
Abun da Sadiya ba ta yi zato ba shine ya faru da ita, farin cikinta ya fara kokarin zama bakin ciki, angonta daga kawai ya bi Abokansa za su tafi shi kuma ya rufe kofa, tsawon awanni bai dawo ba. Ta kwaye gyalenta tare da damuwa, ta zuro kafafuwanta kasa sa’an nan ta mike a tsaye.
“Wannan wanne irin al’amari ne, daga kawai ya ce zai je rufe kofa har yanzu shiru kamar an aiki bawa garinsu.”
Ta fito ta duba, Angonta baya falo, baya kitchen, baya toilet, baya farfajiyar gida , ina ya tafi? Tambayar da kuka ya mata rakiyar laluben amsarta.
.
04:OOam
DAKIN CECELIA
.
Mubarak a kwance yayin da Cecelia ke gefensa, ya tashi a zaune a firgigit ya kai kallonsa kan agogo, bayan nazarta sai ya zuro da kafafuwansa kasa, ya mike ya nufi in da agogo da hularsa suke, dai-dai lokacin da shedaniya Cecelia ta farka. Ta kalle shi tana mutsittsike ido
“Ba dai tafiya za ka yi ba.
”Ai na ma yi kokari, wanne ango ne zai iya irin wannan rashin adalchin a darensa na farko, Allah sarki baiwar Allah yanzu haka tana can cikin zulumi.”
Ya fada ba tare da ya kalle ta ba, ya fara daura agogonsa sa’an nan ya waigo ya ce da ita
”Sai haduwa ta gaba.”
Ta yamutsa fuska.
”Kai, Namiji mugu ne, har yanzu mamakin dalilin da ya sa baka aure ni ba nake.”
.
”Wannan kuma batu ne na qaddara.”
.
“Kaddara ko son zuciya?”
Yayi murmushi kawai.
“Ni kin ga na tafi, sai a lokaci na gaba.”
.
06:50am
DAKIN SADIYA
Sadiya ta kasa zaune ko tsaye, tun tana kuka hart a tsinci kan ta a lokacin da kukan ya ki zuwa, a wannan karon ma da ta dauko wayarta ta gwada kiran lambar Mubarak , amsar daya ce da sauran kiran baya “The number u dial is switch off.” Ta yi jifa da wayar, a Dai dai lokacin da Mubarak ya turo kofar dakin ya shigo, ta daga kanta da sauri ta kalle shi, shi ma ya bi ta da kallo tare da sanyin jiki. Da sauri ta je ta zube a gabansa tana kuka
”Haba Mubarak, wanne irin abu ne wannan? Ashe ba za ka so kwanciyar hankalina ba, ashe za ka iya mayar mini da farin cikina zuwa baqin ciki, ashe za ka iya mayar mini da dariyata kuka, ashe za ka iya mayar da kwanciyar hankalina zuwa tashin hankali, ashe za ka iya mayar mini da daren da nake alfahari da shi zuwa daren da ba na marari, ashe za ka iya mayar mini da gadon aurena makara, a wannan lokacin ban dace na amshi hukunci da kukan baqin ciki ba.”
Ta kuma fashewa da kuka
”Da za ki saurari uzurina da ba ki yanke mini hukuci da bahaguwar fahimta ba.”
“Ba wani uzuri ko dalilin da zai sa ka qi kusantata a daren farkonmu, sai dai ko in dama ba muradinka ba kenan.”
“Kin dai san rai sama yake da komai, to bayan fitar mu sai Abokina Sunusi ya yanke jiki ya fadi. Na san ko ke ce kika tsinci kan ki a irin wannan yanayin abun da za ki yi bai wuce ki kai shi asibiti ba.”
A zahiri a wajen Mubarak ba ceton rai ne sama da komai ba face bukatarsa!

Namiji rigar qaya... Adaibi ahankali...

Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 20:39
In Hausa Novels
Azal Part 3 Title : Azal Part 3
Description : Dan Hajiya ya nufi gadon da Hajiyansa ta ke da sauri ya kama hannunta, sa’an nan ya fashe da kuka. Lokacin da a ka kira shi a ka sanar masa...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Azal Part 3"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ▼  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ▼  March (128)
      • Photos: Musulmi Ya Koma Haushin Kare Bayan Ya Je C...
      • Azal Part 6
      • Azal Part 5
      • Ana Sharrin Tsige Shugaba Kasar Afirka Ta Kudu
      • Photos: Buhari Ya Isa Birnin Washington
      • Photos: Daga Wajen Jana'izar Kanal Suma'ila Inusa
      • Ko Mahaifina Ya Zagi Buhari Sai Na Zage Shi - Wan...
      • Photos: Yan Shi'a Sama Da Dubu Goma Sunyi Zanga-Za...
      • Sojojin Najeriya Sun Hana 'Yan Shi'a Yin Taro A Ka...
      • Gwamnatin Kano Ta Shiga Batun Farashin Ruwan Leda
      • Gobara A Kasuwar Ikom Dake Jihar Cross River
      • Yanda Zaka Sace Zuciyan Yarinya.
      • Anyi Taron Marubuta Litattafan Hausa A Kano
      • Kachikwu Ya Ba Yan Nijeriya Hakuri Akan Matsalar M...
      • Photos: Atiku Abubakar Yayin Ci Abinci Da Yan Gudu...
      • Graphic Photos: Sojoji Sun Katse Harin 'Yan Boko H...
      • An Kashe Hafsan Sojan Da Aka Sace
      • Gaskiya Buhari Ya Yi Matukar Taka Rawar Gani Wajen...
      • Photos: Obasanjo Ya Ziyarci Jihar Borno
      • Bola Tinubu Ya Caccaki Ibe Kachikwu Akan Matsalar Mai
      • Wata Budurwa Ta Sa An Kashe Wani Dan Acaba
      • Photos: Daga Wajen Bikin Producer Kannywood Abdul ...
      • Photos: Sabin Hotuna Rahma Sadau
      • A Daina Sa Wa Gwamnatin Bubari Ido - IBB
      • Photos: Ganduje Ya Ziyarci Kasuwar Sabon Gari
      • El-Rufa'i Da Mataimakin Sa Sunyi Mare-Mare
      • Sheik Sani Yahaya Jingir Na Raye Bai Mutu Ba
      • Gobara Ta Tashi A Kasuwar Sabon Gari A Jihar Kano
      • Photos: Sojojin Najeriya Sun kashe Yan Boko Haram ...
      • Matsayain Zawarawa Da 'Yan Mata A Gwamnatin Ganduje
      • Photos: El-Rufai Ya Gana Da Yan Wasan Super Eagles
      • Boko Haram Sun Sace Mata 16 A Garin Madagali
      • An Daure Adam Johnson Shekara Shida
      • Photos: Anyi Hukunci Ma Wasu Mazinata Uku A Kasar ...
      • Video: Abubakar Shekau Ya Mika Wuya
      • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Kwamitin Da Za Ta Bin...
      • Hukumar Kwastan Ta Sake Hana Shigo Da Shinkafa
      • Allah Yana Fushi Da Buhari - Fayose
      • Majalisa ta zartar da kasafin kudin 2016
      • Gwamnatin Tarayya Za Ta Sanya Naira Bilyan 350 A F...
      • Allah Ya ISA Ban Yafe Ba Part 14
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 15
      • An Zargi Gwamnatin Jihar Bauchi Da Karbar Na Goro ...
      • Video: Sasanta Ganduje Da Kwankwaso
      • A Gaban Idona Sojoji Suka Hallaka 'Yan Uwana Uku, ...
      • Buhari Ya Bukaci Bankuna Su Baiwa Manoma Rance Dom...
      • Sojojin Najeriya Sun Kashe Yan Boko Haram 58 A Kau...
      • Gwamnatin Buhari Ta Kwace Kadororin Tsofin Gwamnon...
      • Hukunci Wanda Ya Kashe Dan Fashi
      • Graphic Photos: Barayin Shanu Sun Kashe Mutane 20 ...
      • Photos:Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Daidaita Tsa...
      • Photos:Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Daidaita Tsa...
      • Yan Shi'a Sun Gurfanar Da Sojojin Najeriya Gaban K...
      • Majalisar ASA Na Shirin Yin Fito Na Fito Da Buhari
      • Budaddiyar Wasika Zuwa Ga Gwamna Jihar Bauchi
      • Ali Nuhu ya mika kyautar Tijjani Ibrahim
      • Wayar Sakataren Majalisar Musulunci Ta Duniya Ta Y...
      • Izala ta Karyata Jita-Jitar Sace Wayar Shaihun Mal...
      • Photos:Gwamna Jihar Kogi Tare Da Matan Sa Uku
      • Abu Daya Ya BamBanta Mulki Buhari Da Na Fir'una - ...
      • Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wani Kwamishina Na J...
      • Yan Bindiga Sun Halaka Mutane Da Dama A Jihar Zamfara
      • Gwamnatian Jihar Borno Ta Rushe Kantomomin Kananan...
      • Gwamnatin Kano Ta Sake Baiwa Wata 'Yar Fim Din Hau...
      • Azal Part 1
      • Azal Part 2
      • Azal Part 3
      • Azal Part 4
      • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Yi Afuwa Ga Fursunoni 56
      • Ganduje Ya Caccaki Kwankwaso
      • Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe Mutane 22 A Wani Ma...
      • An Gano Ma'aikatan Bogi Dubu 22 A Jihar Bauchi
      • Photos: Buhari Ya Isa Kasar Equatorial Guinea
      • Kasar Masar Ta Tsige Ministanta Kan Batanci Ga Ann...
      • Photos: Daga Wajen Bikin Kannywood Award
      • Bama-Bamai Sun Tashi A Cameroun
      • Kungiyar Matasa Magoya Bayan Buhari Sun Karrama Ba...
      • Ganduje Na Shirin Kai Kwankwaso Gaban EFCC
      • Harin Bam Din Kunar Bakin Wake Ya Raunata Sojoji U...
      • An Dawo Da Ruwan Sha Na Dauri A Jihar Sokoto
      • Yar Amana Part 15 (Karshe)
      • Graphic Photos: Mutane 18 Sun Rasa Ransu Sakamakon...
      • Ana Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da 'Yan Boko Hara...
      • Yar Amana Part 14
      • Na Karbowa Faruk Lawan Dala Dubu 100 Daga Wurin Ot...
      • Yar Amana Part 13
      • Aljanu Basu Son Azkar Din Safe
      • Photos: An Kashe 'Yan Boko Haram Da Dama A Jihar B...
      • Ina Sane Da Mawuyacin Halin Da Ake Ciki A Kasar Na...
      • Photos: Ministan Kwadago James Ocholi Ya Mutu A Ha...
      • Yanda Zaka Saya 1GB Da 3GB Akan N200 Da N500 A Lay...
      • Yar Amana Part 12
      • Hukumar SSS Ta Kama Masu Yi Wa Boko Haram Safarar ...
      • Yunwa Da Matsin Lamba Ta Soma Sanya 'Yan Boko Hara...
      • An Gano Iyayen Yarinyar Da Ta Bace A Tsakanin Kadu...
      • Maganin Matsalar Ciwon Fitsari
      • Yar Amana Part 11
      • **AL‘AJABI part 20*
      • Al'ajabi Part 19
      • Gwamna Ganduje Na Kano Ya Yi Rashin Mahaifiyarsa
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ►  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ►  November (308)
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...
  • Yadda Kotu Ta Daure Bobrisky Watanni Shida Ba Tare Da Zabin Biyan Tara Ba
    Kotu ta daure Bobrisky watanni 6 ba tare da zabin biyan tara ba Babbar kotu a jihar Lagos ta yanke hukunci ga Idris Okuneye da a...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger