1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5

Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5

By Abdul Mk
Add Comment
Wednesday, 13 April 2016


.
To da yake Amatu ba ta tanka mata ba sai ta wuce zuwa ban daki, ranta a bace, dama haka abin yake, in mutum ya shirya fada da kai fita harkarsa don kar ku lalace gaba daya, shurunta kuwa ya yi amfani, can dai ta dawo da sauri ta dauki jakarta "Har ina manta wa da jakata" in ji Mari, haka suka yi watsi da ita ba wanda ya ce mata "Ci kanki!" dan lokaci kadan Jummai ta daga kai tana kallon Amatu "Sai fa kin yi haquri da Mari, don ko dan giya bai kai ta buguwa ba, yanzu sai ta birkice miki ki rasa kanta, ko da yake ku take wa wannan shaqiyancin, amma ni ai ina, tunku ya san shurin da yake wa kashi"
.
Amatu ta dan yi quta "Q!" tana duban in da Mari ta shiga "To wai me ya sa mu ne kadai take wa wannan cin kashin, ke kuwa duk abin da kika yi mata ba ta iya ce miki komai? Ni fa ba ni na kar zomon ba rataya aka ba ni, wannan ai shi ne na dan Fulani: Mai raha yi raharka, mai dariya ka ga na ka! Ke da ba da labari, ni da daukan laifi" Jummai ta dan daki Amatu kadan a cinya ta ce "Ba ni nake raka ta wurin samarinta ba? Ba abin da ban sani ba nata, in na tubure mata dole za ta nemi sulhu"
.
Har Amatu ta yunqura za ta miqe sai kuma ta dawo ta zauna "Ban tambaye ki ba? Dazu kin dauko zancen Mr KB sai kika yanke, ca nake shi ne kadai ya tsane ta a duk cikin lakcarorinmu? Kullum fa zaginsa take yi in muna hira, kuma shi ma da ta fara masa rashin kunya zai kore ta daga ajin" "Wa din?" "Mr KB mana" "A ganinki?" "A ganin kowa ma, don ko jiya na ji an ce ya kore ta" Jummai ta qyalqyale da dariya, ta dan waiwaya ta kalli hanya, sannan ta saukar da murya ta ce "Kar fa ki yarda wani ya ji ... wallahi soyayyarsu suke sha!"
.
"Ban gane ba!" In ji Amatu, Jummai ta ce "To ki lura, ai dazu na gaya miki irin shigar banzan da take yi a duk ranar lakcarsa" "A! Ba raina shi ta yi ba? Ca nake rashin kunya take yi masa, shi kuma yana qoqarin yi mata magana, shi ya sa take haka don ta baqanta masa rai, ba ta san kuma saba wa mahalicci take yi ba" Amatu kenan, "Mhn" in ji Jummai "A fahimtarku ba? Amma gaskiya da walakin domin in ya kore ta cewa yake yi ta jira shi a ofis, to mu dauka ba hira suke yi ba, kin taba ganin ta fadi ko da test dinsa bare exam? Me ya sa bai taba kai qararta wurin wani ba?"
.
Amatu ta yi shuru tana tunani, kamar dai tana taro abubuwan da suka riqa faruwa a baya, Jummai ta ci gaba da cewa "Ko exam dinsa za a yi ita take fara fita, kuma bata taba samun qasa da B ba, amma ita da ba ta da note dinsa kuma ba ta cika zama period dinsa ba ya za a yi ta riqa cin jarabawarsa? Ni ba na zargin ta da komai, ko na ce suna yin wani abu, amma ba shakka irin siyasar duniya dinnan ce, ki ji qasa da qasa suna zagin juna har ana qona tuta da zanga-zanga da atisaye kala daban-daban amma har ki gama rayuwarki ba za ki taba ganin yaqi a tsakaninsu ba, sun fi kowa zaman lafiya.
.
Amatu ta dan yi murmushi ta ce " Ok rigimar Isra'ila da Iran ba? Kullum cikin zagin juna ne, amma alaqarsu ta fi ta kowa gyaruwa, to amma in ta yi wari za mu ji... ya maganar Yakubu? Tun da muka tattauna sau daya ban sake ganinsa ba!" Jummai ta dan kalle ta da gefen ido tana dariya, "Hajia Amatu, ya sami shiga ne na yi masa albishir?" Ta ba ta amsa cikin sauri "No kin gane ko? Ba na son ya ga kamar na wulaqanta shi ne kin gane? Ban bude masa fuskata ba, wato ni da ina so ya zo gidanmu ne tukun albashi ma san juna a can, kin ga irin wannan wurin kin gane ko? Sai ya zama kamar kamar..."
.
Jummai ta katse ta da cewa "Kin gane ko?" Amatu ta kai mata duka, Jummai ta sa hannu ta tare "Ni dai kun mai da ni jaka, wannan ta tafka wancan ma haka, to yanzu me kike so a yi? Kin gane ko?" Amatu ta dan yi dariya "A'a in da zai zo gidanmu sai mu tattauna sosai yadda za mu san juna, kin ga nan gaskiya galibin alaqoqin da ake yi ba su cika qarko ba, samarin yanzu sun faya son kansu"
.
Wannan hirar dai dole ta yanke tun da Mari ta dawo "Na wanke kwalliyar don masharranci ya ji dadin qararwa" in ji ta, Amatu ta dan yi murmushi "Mari manta da Jummannan kawai, ita fa in ba ta tsokani mutum ba hankalinta ba kwanciya yake ba, ko da yake wani lokacin takan yi qoqarin fadin gaskiya, Mari yaushe za ki ziyarce ni?" "Mhn, akwai wani wa'azin qasan ne?"
.
Suka qyalqyale da dariya "Allah ya shirye ki Mari, ni ba wa'azi zan yi miki ba, ji na yi kikan ziyarci Jummai, ban da wannan ma mu kullum muna tare amma qafarki ba ta taba taka gidanmu ba, kin san kuwa zumunci bai ce haka ba" Mari ta sami wuri kusa da qarshen benci ta zauna tana kallon wani wuri.
.
"Ku ai ba zuwa gidan malamai ne matsala ba, a riqa maka kallon wani fandararre, shi ne problem din, gaskiya in dai kina so ki zo gidanmu mu kowa na mu ne ba ruwanmu da rayuwar wani, kowa ta kansa yake yi"
.
"Wai yaushe muke da class ne? Ni fa na gaji da zamannan wallahi" maganar Jummai kenan, tana yatsina fuska kamar wace take hira da saurayi, ta wuce sa'a daya tana taunar cungam guda daya, sai tauna shi take yana qara, wani sa'in ma ta huro shi kamar balam-balan, Amatu ta ce ko kin manta ne? AA ba zai so ba sai qarfe Hudu daidai, kin san shi dan qa'ida ne, sai dai abin da yake burge ni da shi ba ya fita sai ya kammala darasinsa kuma zai yi wahala ka ga an qosa ya fita, kowa yana son koyarwarsa"
.
"Ko dai...." In ji Mari Amatu ta kalle ta "Ba za ki gane ba, ni ai kin san principles dina a kwalejinnan ba kowa nake kulawa ba, duk da na san cewa ba wai na fi kowa kyau ne ko mahaifina wane ba, amma kin san wani abu?" Mari ta zuba mata ido, amma ba ta tamka mata ba, ita kuwa ta ci gaba da magana "Mu dinnan da kike gani kamar kwano ne da aka zuba wani abu a ciki ana so a sayar, in kina so a ga darajarsa to ki rufe shi, wanda suka san shi za su tabbatar qudaje ba su bata shi ba, wadan da kuma ba su san shi ba za ki ga ba abin da suke so sai su ga me ke cikinsa har da ake rufewa?"

Daga, Muhammad Alkasim

Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 11:05
In Hausa Novels
Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5 Title : Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5
Description : . To da yake Amatu ba ta tanka mata ba sai ta wuce zuwa ban daki, ranta a bace, dama haka abin yake, in mutum ya shirya fada da kai fita h...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ▼  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ▼  April (89)
      • Photos: Ga Abunda Yafaru Da Shi Bayan Yazagi Buhari
      • Photos: Dogara, Amaechi, Da Wasu Gwamnoni A Bikin...
      • Ina Bala'in Sonki
      • Photos: Matsalar Man Fetur: Bature A Cikin Bas
      • Labarin Wani Saurayi Mai Chatin Da Wata Budurwa
      • Photos: Sabin Hotuna Maryam Booth
      • Stella Oduah Ta Saci Naira Bilyan 3.6 - EFCC
      • Photos: Maciji Da Na Kashe A Kofar Gidan Mu
      • Photos: Yayin Da Biri Ya Ga Kyakkyawan Yarinya
      • Photos: Sarkin Kano Da Yar Shi
      • Photos: Sojoji Sun Kama Wasu Shugabannin Boko Haram
      • Dole Ne Yuguda Ya Bi Ka'idojin Jam'iyyar APC Idan ...
      • Babu Sanatan Da ya Rako Saraki Zuwa Kotun CCT A Yau
      • Me Ke Faruwa Tsakanin Tiwa Savage Da Mijinta
      • Photos: Aisha Buhari Ta Ziyarci Jihar Ibadan
      • Daga Hamsin Zuwa Biyu: Sanatoci Biyu Ne Suka Rako ...
      • EFCC Ta Gano Dala Bilyan 12.9 Na Makamai
      • Photos: Sojoji Na Ci Gaba Da Kakkabe Sansanin 'Yan...
      • Photos: Sabin Hotuna Adama Indimi
      • Uwar Gida Marigayi Mamman Shata Ta Rasu
      • Photos: Sabin Hotuna Zainab Indomie
      • Graphic Photos: Hmm..Wata Macce ta yakewa Mijinta ...
      • Za A Hana Bara A Jihar Sokoto
      • Zafin So Part 1
      • Mahassada Ne Ke Neman Bata Mini Suna - Sani Danja
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 6
      • Photos: Sabin Selfie Na Zahra Buhari
      • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
      • Wasu Al'ummar Nijeriya Sun Soma Kira Da A Rufe Maj...
      • Matar Shugaban Hukumar Shige Da Fice Ta Kasa Ta Wa...
      • Yan Daba Sun Yi Yunkurin Halaka Wani Matashi A Kano
      • Adesola Amosun Ya Dawo Da Naira Bilyan Biyu - EFCC
      • Graphic Photos: Masu Safarar Kaya Sun Illata Wasu ...
      • Video: Matasa Sun Jefi Sanata Isa Hamma A Garin Ni...
      • Photos: Sabin Hotuna Fatima Yola
      • Yan Danfara Na Amfani Da Suna Ali Nuhu
      • Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wani Ma'aikacin Mata...
      • Photos: Atiku Tare Da Matarsa A Wajen Bikin Dan Sa
      • Amurka Zata Maido Da Kudaden Abacha Najeriya
      • Amurka Zata Maido Da Kudaden Abacha Najeriya
      • Photos: Dan Atiku Abubakar Ya Auri Yar Ghana
      • Photos: Daga Wajen Bikin Littafin Aisha Buhari
      • As-Sheikh Muhammad Ayyub Limamim Masallacin Annabi...
      • Jihar Nassarawa Na Cigiyar Gwamnansu
      • Photos: Aisha Buhari Ta Ziyarci Jihar Borno
      • Sabon Hanyoyin Dan Yan Boko Haram Suke Kai Hari
      • Babu Laifi A Bashin Da Buhari Zai Ciwo - Garba Shehu
      • Yan Sandan Kaduna Sun Bindige Wani Matashi Dan Bun...
      • Goron Jumma'a Daga Mai Martaba Sarkin Bauchi (Dr) ...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Shugaban St...
      • Hukuncin Zuwa Wajen Yan Duba
      • Abubuwa Da Kan Haifar Da Cutar Bugun Zuciya
      • Al'ajabi Part 23 {Karshe}
      • Al'ajabi Part 22
      • Al'ajabi Part 21
      • Al'ajabi Part 20
      • Al'ajabi Part 19
      • Photos: Boko Haram Sun Sake Sabin Hotuna Yan Mata ...
      • Daga Jama'a: Yau Na Gamu Da Abin Al'ajabi
      • Gajeren Tarihin Sheikh Jafaar Mahmoud Adam
      • Wacce Irin Nasiha Kike Wa Yar Ki Lokacin Aurenta
      • Sheikh El Zakzaky Da Zeenatu Suna Cikin Mawuyacin ...
      • Photos:Sabin Hotuna Yar Osinbajo Kiki
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Yan Najeriya A China
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 11
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 13
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 12
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 10
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 9
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 7
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 4
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 5
      • Akwai Kyakkyawar Makoma Game Da Hadin Gwiwa Tsakan...
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 3
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 2
      • Allah Ya Isa Ban Yafe Ba Part 1
      • Majalisar Jihar Nassarawa Ta Tsige Membobinta Guda...
      • Photos:Buhari A Kasar China
      • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Tabbatar Da Mutuwar Muta...
      • Fati Nijar Tayi Wakoki Wa Janar Burutai
      • Photos:Bayan Kwana Biyar A Amurka, Buhari Ya Iso N...
      • Al'ajabi Part 5
      • Mawaki Sani Aliyu Dandawo Ya Rasu
      • Real Madrid Ta Doke Barcelona Da 2-1
      • Azal Part 8
      • An Rantsar Da Muhammadou Issoufou
      • Azal Part 7
      • Kiran A Saki Zakzakiy Rashin Kishin Qasa Ne - Baba...
      • Photos: Faston Da Ya Binne Mutum A Tushen Gininsa ...
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ►  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ►  November (308)
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...
  • Yadda Kotu Ta Daure Bobrisky Watanni Shida Ba Tare Da Zabin Biyan Tara Ba
    Kotu ta daure Bobrisky watanni 6 ba tare da zabin biyan tara ba Babbar kotu a jihar Lagos ta yanke hukunci ga Idris Okuneye da a...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger