1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Kazamar Gida Part 5

Kazamar Gida Part 5

By Abdul Mk
Add Comment
Saturday, 7 November 2015
Anti Habiba salati takeyi tana k'arawa lokacin data gama sauraron maganganun da suke fitowa daga bakin Jafar.
"Wannan abu dame yayi kama? Amma kuwa Siyama ta bani kunya,inajin wai wai a bakunansu Husna(d'iyarta)kafin aurenku ashe gaskiyarsu suke fad'i? Eh lallai Siyama ta cika KAZAMAR GIDA."
Jafar ya dubi Antinsa da mamaki
"Oh anti,har su Husna sun sani amma babu wanda ya tab'a sanar dani?"
Ta harareshi
"Tayaya za'a sanar maka kakana? Ni kaina ban yarda ba da suka sameni da zancen. Koda ma an fad'amaka yanda ka zama majnunu Siyama ai ba yarda zakayi ba. Ko ka manta furucinka a baya na tuna maka? Cewa fa kayi Siyama ta mamaye dukkanin b'angarorin dake jikinka. Toh waye mai karambanin tarar ka da wannan zancen kakana?"
Ya tuntsire da dariya,daman yasan muddin ya kawo laifin Siyama wajen antinsa zaiji magana tunda har da ita cikin masu bashi shawarar ya hakura da ita alokacin da Hajiyar Siyama ta hura wutar kiyayyarta ga auren nasu. Amma ina! Son da yake yiwa Siyama bai bari yaji shawarar kowannensu ba. Ga kuma rabo daya riga ya rantse.
"Oh antina,nikam na kawo kaina. Nidai a taimakamin da mafita abar tuna baya."
Ta tab'e baki
"Zanje gidan naka,nafison na ganewa idona kafin musan abunyi idan ta kama sai mu maidata makaranta." Ta k'arashe da wasa.
Jafar ya k'ara sanya dariya,
"Haba anti,yarinyar da tayi hadda? A dai nemo wani hanyar."
"Shikenan zan zaunar da ita muyi magana,Allah Yasa a dace."
"Amin amin antina."
Ya jima a gidan anti habiba suna hirarsu da dariya domin antin tasa badai raha ba amma fa sam bata da kyau yayinda aka tab'ota. Tana da zafi ainun.
********
Misalin uku da rabi na ranar Talata. Siyama tana zaune a tsakar gidanta ta bararraje tana aikin karatun wani sabon littafi wanda takanas taje bakin asibiti ta siyo,tana yi tana taunar cingam abinta. Zanin atamfa ne a jikinta da bak'ar T-shirt,kanta ko dankwali babu.
Gefenta kayan wanke wanke ne tuli guda k'uda yana ta zarya akansu.
Daga d'aki kuwa,almajirinta Dauda ne ke faman shara bisa umarnin uwardakin tasa.
A haka Anti Habiba tayi sallama ta shigo gidan. Siyama ta mike da sauri,tabbas saida gabanta ya fad'i ganin anti habiba a daidai wannan lokacin da bata tab'a tsammani ba. Ta hau kame kame
"Wa alaikissalam,oyoyo anti. Ashe kina tafe amma Jafar bai sanar dani ba. Sannu da zuwa."
"Jafar?"
Anti Habiba ta nanata a ranta,suna ne mai girma a zuri'arsu tunda ya kasance sunan mahaifin Hajja. Ashe har a yanzu akwai matan dakan iya kiran sunan mijinsu gatsal basu ko jin nauyi a bakinsu?
Tana amsa gaisuwar Siyama tana k'arewa gidan kallo,ko iyakar wannan sun isa a kira Siyama KAZAMAR GIDA. Mamaki takeyi na yanda gidan mutum ke a haka har ma ta iya d'aukar littafi tayi zaman karatu.
"Anti ya kika tsaya? Ki shigo ciki."
Anti habiba ta jinjina kanta,ta cusa kanta a falon,daidai lokacin da Dauda ya kwashe shara ya fito daga k'uryar d'akin Siyama.
"Na kammala Hajiya,sauran ina?"
Siyama ta dubi anti habiba wacce ta zuba mata ido tana sauraron abunda zata ce. Ta dubi Dauda tana 'yar dariyar borin kunya
"Uhum,kayi wanke wanken tukunna."
Bayan fitar Dauda,anti habiba ta girgiza kanta ta soma magana cikin tsabagen takaici.
"Haba Siyama! Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Siyama kin bani kunya. Ashe haka kike? Kaiconki Siyama,menene amfanin iliminki? Gidanki kaca kaca ace har kina da damar daukar littafi kiyi zaman karatu? Kafin ma akai ga littafi,ki k'arewa jikinki kallo daga sama zuwa k'asa ai ko wata jahilar ta fiki kyawun duba. Uban me kike d'auka a karatun? Wane darasi ne aciki dake nuna ayi rashin tsafta? A baya koda kud'i aka cemin na yarda zaki aikata wannan shiriritar ni Habiba bazan amince ba! Inayi maki kallon 'yar kwalliya kuma 'yar kwalisa,menene dalilinki na chanja akalar rayuwarki yanzu? Ace almajirinki shine zai maki dukkan ayyukan gida? Ina laifin ma sharar tsakar gida da cefane,amma ina shi ina tsallake falonki har ya taka zuwa k'uryar d'akinki sirrinki?!"
Siyama duk ta tsure,tasan anti habiba bata dakyau wajen fad'a,ai kuwa sai yi takeyi babu kakkautawa. Tun Siyama tana durkushe har ta zauna ta soma sheshshekar kuka.
Karshe kuma ta shiga nasiha.
"Tsafta takan k'arawa mace daraja ta musamman a wajen mijinta. Babu namijin da a duniya zaiso rashin tsafta. Toh ni yanzu abunda yafi dauremin kai shine,tayaya kike ibada? Kina sane kuma kin karanta a makaranta komai na addini baya tafiya saida tsafta ko? Zaman aurenki ya sunansa?"
Anti habiba tana girgiza k'afa tayi kwafa
"Tab! Siyama kina da aiki."
Ta fad'a tana girgiza kanta,can ta k'ara dubanta fuska a yamutse
"Batun girki kuma fa Siyama? Kina kokarin yiwa mijinki?"
Siyama tana mutsistsika idanunta sai lokacin ta samu karfin gwuiwar tankawa
"Inayi anti amma Jafar bai damu da cin abincina ba."
Anti ta fusata
"Kika k'ara ambaton sunansa a gabana wallahi sai bakinki yayi jini yanzun nan! Ke ba abun kunya bane ki dunga kiran sunan mijinki babu sakayawa ba komai? Kai wallahi nayi tirr da halayenki. Ko a litattafan da kike karantawa banda kiji ana kiran honey,darling sweety ko kuma baban wance ko wane bakijin komai! Badai ki tsinci mace mai tarbiyyar arziki ba tana kiran sunan mijinta ba Siyama. Yanzu haka babu alamar jikinki yaga ruwa. Ji gashinki yanda yake tamkar dambun da babu mai. Gida babu gyara babu komai,a haka wane namiji ne zai so ya zauna har ya ci abincinki? Allah Yasa ma kin iya girkin ba jagwalgwalo kawai kikeyi ba."
Anti Habiba ta cigaba da yi mata nasiha mai ratsa jiki har tana tsoratata akan matukar bata gyara ba toh fa wataran a kwana a tashi Jafar aure zaiyi.
Bata bar gidan ba saida ta sanya Siyama a gaba ta gyara komai tana taimaka mata. Ta tsaya a gabanta har tayi girki anti tana fadan ai data dunga daukar litattafan soyayya gwara ta nemi na koyon girki. Ta sanyata tayi wanka,a wajen sutura ma abu ya gagara. Yawancinsu duk riguna ne zanin sun kod'e. Masu kyawun kuma babu wanki. A karshe dai dakyar aka samu riga da wando marasa nauyi ta sanya.
Bayan kammalawa anti ta dubi ko'ina, babu sauran gyara,sannan ta kalli Siyama.
"Toh yanzu ko kefa Siyama,kin koma tamkar wata sarauniya. Inda haka mijinki yake tarar dake tsaf tsaf me zai sanyashi fargabar dawowa gida akan lokaci?"
Siyama tayi murmushi tana sunne kanta k'asa,a karshe anti tayi mata sallama ta tafi bayan tayi mata alk'awarin aiko mata da spices da litattafan girke girke na boko dana hausa....!
Tun shigowarsa yake bin ko'ina na farfajiyar gidan da kallo. Ganin da yayi ko'ina fes sai k'amshi ke tashi ya fahimtar dashi antinsa tazo. Murmushi ya saki yana duban sararin samaniya yanda ake walkiya da iska mai ni'ima da sanyi. Fatansa Allah Yasa rayuwarsu ta d'aure a haka.
"Barka da zuwa."
"Unbelievable!"Jafar ya fada a ransa,ya d'ora da hamdala. Kallonta yakeyi tun daga sama har k'asa,tayi masa kyau sai k'amshi ke tashi daga jikinta.
Mamakinsa bai k'aru ba saida tasa hannu ta karb'i ledar hannunshi.
"Bismillah mana." Siyama ta fad'a,nauyi sosai takeji ta k'ara kiran sunan nashi hakanan tana jin kunyar kiransa da wani sunan da bata saba da bai saba jin ta kirashi dashi ba. Ta gwammace ta bar kiransa kwata kwata,gwara tayi zancenta kai tsaye.
Ya bi bayanta,har kofar d'akinsa. Ya mik'a mata mukullin da yake had'e dana mashin d'insa. Ta karb'a ba tare data dubeshi ba domin idanuwansa har lokacin sun gaza barin kallonta. Bayan sun shiga,Siyama ta taimaka mishi wajen rage suturar dake jikinsa. Jafar jinsa yake tamkar ba shi ba. Yana murmushi yace
"Nagode,ya babynmu?" (Kuji fa,yau Jafar harda tambayar baby?!)
Murmushin itama tayi alokacin da yake tab'a cikinta.
"Lafiyarsa kalau,bebin da ake mantashi?'
Dariya yayi yana mai juyawa ya fita, ganin ya nufi kicin tayi saurin dakatar dashi cikin sassanyar murya
"Ai na dafa maka ruwa na had'a,yana band'akina."
Duk da yasan bazai taddashi da kazanta ba yau,hakan bai hanashi jin fad'uwar gaba ba. Ya bita a baya har d'akin,band'akin a wanke a bushe tsaf. Yayi wankansa ya shirya,a'a, sai ya k'ara cin karo da lafiyayyen abinci an jera mishi. Ya zage yaci sosai,ita kanta ta lura yau mijin nata yafi koyaushe farin ciki.
Daren ranar sun farantawa juna,fatan Jafar bai wuce Allahu Yasa Siyama ta d'aure a haka ba. Baisan har yanzu akwai sonta mai yawa haka a ransa ba sai a wannan daren......!
"Nifa ba don komai na damu dashi ba,abunda kike zargi don Allah ki bari. Kwanansa goma sha shida fa rabon da ya ziyarci shagonmu koda da niyyar gaisuwa ce. Shiyasa na damu amma ba don komai ba."
Ladi ce ke wannan zancen,kanta akan cinyar Mahaifiyarta.
Mama tayi dariya
"Yanzu menene ya kawo dogon bayanin nan? Toh naji ba sonshi kikeyi ba,saidai kin damu dashi ko?"
"Eh,a matsayinsa na yayana."
Mama ta girgiza kanta tana mai tufkewa diyarta ta gashi
"Au haba,ashe yayanki ne? D'an babanki ne ko d'ana?"
Ladi ta mike zaune tana turo baki cike da shagwab'a
"Toh mutunci fa mukeyi,kema kinsha cewa yana da mutunci. Tayaya zaki had'a irina da namiji irinsa?"
Ta langab'ar da kai tana tab'e baki cikin sanyi tace
"Yafi k'arfina,ya kere ni Mama. Irinmu sai marasa gata."
Mama taji tausayin diyarta ya tsirga mata zuciya,ta kamo hannunta
"Waya fadamaki Sarah? Kina da Allah. Hakanan ni mahaifiyarki ina tare dake. Ba don ma mutuwa mai raba tsakani ba,da yanzu mahaifinki yana nan tare damu. Sannan ke ba macen k'i bace,bamu da kud'i bamu da kyau. Amma zuciyoyinmu masu kyau ne. Watarana zakiyi mamakin mijin da zai nemi aurenki Hadiyya. Kada ki dauki zancena a hagunce,ba lallai sai mai kud'i ba,kodayaushe addu'a na Allah Ya kawo maki mijin da zai jib'anci al'amuranki,zaibaki kulawa har karshen rayuwarsa."
Ladi ta sunkuyar da kanta tana murmushi
"Allah Yasa mamana."
"Amin Hadiyya. Don haka ba Jafar ba,sai kiga Allah Ya had'aki da wanda yafi Jafar. Ai shi Allah babu ruwansa da kud'i ko talauci,matukarYa kaddaro zaka auri mutum koda ace shine sarkin masu kud'in duniya,ko kuma shine wanda yafi kowa talauci."
Ladi ta jinjina kanta,tabbas gaskiya Mama ta fad'a. Ta damu da lamuran Jafar,hakanan tana tsoron ya kasance wannan yanayin da takeji a zuciyarta game dashi shine SO. Ambaton hakan saida gabanta ya fad'i.
Ta k'ara maida kanta cinyar mama idanuwanta a lumshe,murmushidauke akan fuskarta.
"JAFAR"
Ta maimaita sunan cikin ranta,a hankali ta soma ayyano kamanninsa. Dogo ne,baya daga layin kyawawa saidai bazaka kirashi mummuna ba. Yana da cikar suma,bashi da wani hanci saidai masha Allah akwai idanuwa.
Ta muskuta tana murmushi har a lokacin,duk shigar da Jafar zaiyi ita kam burgeta take. Bata fiye ganinsa da kananun kaya ba sai jefi jefi. Toh a ajiye duka wadannan ma a gefe,haka kawai take kaunarsa. Halayensa sukan burgeta matuk'a. Bashi da girman kai,baya daukar duniya da zafi. Yakan dauki kowane mutum da daraja,baya kyashin bawa kowa girmansa matukar ya girme masa. Wannan yasa shima mutane kan ga mutuncinsa sosai,ciki kuwa harda ita. Bata tab'a cin karo da namijin da ya burgeta ba irinsa. Kodayaushe bata sakarwa customers fuska,don batason abunda zai janyo wani cikinsu ya gayamata zancen banza kamar yanda wani ya tab'a gigin yi. Tun daga lokacin ta chanja fuska.
Jafar kuwa yawan zuwansa ne ya sanya ta saba dashi,saida ta lura shi d'in kamilin mutum ne sosai kuma yakan girmama mamanta. Abunda ya janyo mishi samun matsayi babba a zuciyar Ladi....!!!!
********
yanxu akasoma..!
Please like Us On   Facebook
Follow us on   Twitter


Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 14:41
In Hausa Novels
Kazamar Gida Part 5 Title : Kazamar Gida Part 5
Description : Anti Habiba salati takeyi tana k'arawa lokacin data gama sauraron maganganun da suke fitowa daga bakin Jafar. "Wannan abu dame ya...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Kazamar Gida Part 5"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ▼  November (308)
      • Kafin Kayi Barci
      • Yanda Ake Hada Lemon Juice
      • Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Banburaitai
      • Photos: Buhari Ya Isaa Paris Dan Halartar Taron Sa...
      • Ana Ta Samun Nasarar Kwato Shanun Sata a Kano
      • Zargin Kinshiyoyin Ta Sun Mata Asiri
      • Al'ajabi Part 16
      • Hisbah Ta Kama Wani Dan Sanda Da Yi Wa Budurwa Ciki
      • An kaiwa 'yan Shi'a hari a Masallaci a Bangaladash
      • Video: Download Highlight Leicester City 1 Manches...
      • Video: Download Highlight Barcelona 4 Real Sociedad 0
      • Yanda Ake Hada Cake
      • Photos: Yusuf da Zahra Buhari Su Halarci Taron Yay...
      • Photos: Sabin Hotuna Shahida Sanusi Lamido Sunusi
      • Buhari Ya Nada Sabun Alkalai
      • Al'ajabi Paart 15
      • Yan Boko Haram Na Shirin Kaima Abuja Hari
      • Mummunar Shiga Mai Bayyana Tsaraici Da Yan Uwa Mat...
      • New Music: Inda Rai Darabo By Hussaini Danko
      • Graphic Photos :Adadin Mutanen Da Su Ka Rasu A Har...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Atiku Abubakar
      • Graphic Photos:Yanayi Wanda Ya Kai Hari Yau A Jiha...
      • Tafsir: Rikicin Duniya Da Na Lahira By Sheikh Isa ...
      • Hanyoyin 25 Masu Sauki Domin Samun Lada Mai Yawa
      • New Music: Kana Raina By Hussaini Danko
      • Bom Ya Tashi Dan Yan Shi'a 15 A Kano
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Sarauniyar Ingila A Malta
      • Tafsir: Tambayoyi Tara Bayan Mutuwa By Sheikh Isa ...
      • Graphic Photos: Wani Dalibi Poly Ya Kashe Kansa
      • Buhari Na Neman Jefa Kasar Nan Cikin Mummunan Hali...
      • Yadda Wani Attajiri Ya Yi Wa Kansa Yankan Rago A J...
      • New Film: Zurfin Ciki 2015 Part 2 Starring Ali Nuhu
      • Yan Najeriya Sun Nuna Bacin Ransu Da Buhari
      • Dan Marigayi Audu Abubakar Ne Zai Maye Gurbin Sa A...
      • Kotu Ta Hana Wata Ma'aikaciya Sanya Hijab A Faransa
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Malta
      • Photos: An Kaddamar Da Sarkin Kano Mastayi Sabon C...
      • Photos: Gwamna Jihar Nasarawa Ya Kwanta Akan Katif...
      • Nafisah Abdullahi Tayi Allah Wadai Da Matan Da Ke ...
      • Photos: Happy Birthday Haleema Atete, Ga Sabin Hot...
      • New Film : Zurfin Ciki 2015 Part 1 Starring Ali Nu...
      • An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambia
      • Magajin Garin Kano Ya Rasu
      • Photos:Buhari,Osinbajo, Saraki, Tinubu Da Amaechi ...
      • Video: Manchester United 0 PSV 0
      • Video: Shakhtar Donesk 3 Real Madrid 4
      • Yanda Ake farfesun kifi
      • Yanda Ake Karya Sihiri Da Lalata Sharrin Aljanu
      • Photos: Buhari Ya Halarci Wajen Binne Matan Awolowo
      • Za A Fara Kama Masu Boye Fetur A Najeriya
      • Abu Ashirin Da Mata Ke So
      • Macen da Aljanna ta fi Karfin ta
      • New Music: Nayi Kira By Hussaini Danko
      • New Music : Kira Nake by Hussaini Danko
      • Yanda Ake Hada Kunu Aya
      • Al'ajabi Part 11
      • Paparoma zai je Kenya
      • An gano wata jigidar bama-bamai a Paris
      • Bangladesh ta haramta amfani da Facebook saboda Tsaro
      • Graphic Photos: Abunda Kishiyarta Ta Mata Ranar Am...
      • Hanyoyin 15 Da Zaka Bi Domin Gujewa Aikata Zinna
      • Al'ajabi Part 13
      • Al'ajabi Part 12
      • Video: Barcelona 6 Roma 1
      • Video: Arsenal 3 Dinamo Zagreb 0
      • Video: Maccabi Tel-Aviv 0-4 Chelsea
      • Photos: An Ba wa 2face Sarauta A Kaduna
      • Buhari Ya Bada Sakon Ta’aziyya Ga Iyalan Audu
      • APC Za Ta Tsayar Da Sabon Dan takara
      • New Music: Mafita By Hussaini Danko
      • New Music: Rabin Mutum By Hussaini Danko
      • Al'ajabi Part 14
      • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
      • Graphic Photos: Wata Yarinya Tana Bukatar Taimako ...
      • Hakurin Zama Da Mace Mara Biyayya
      • Photos: Aisha Buhari A Offishin FIRST LADY
      • Photos: Major AL Ayangbesan, Soja Najeriya Wanda B...
      • Boko Haram, ISIS, Al-Qaeda Na Shirin Kai Hari — Am...
      • Photos: Sabin Hotuna Iyalan Marigayi Sani Abacha
      • New Music: Shakuwa By Hussaini Danko
      • Photos: Buhari Ya Halarci Taron Kasashen Masu Arzi...
      • An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh
      • Darussa Bakwai Game Da Rasuwar Dan Takarar Gwamna...
      • Photos: Isar Buhari Iran
      • Abunda Dokar Zabe Tace Akan Mutuwar Audu
      • An yi jana'izar Abubakar Audu
      • Mutane 8 sun mutu a harin Maiduguri
      • Film: Download Hausa Shargalle Part 2 Starring Sul...
      • Photos: Adama Indimi A Sabon Hotuna
      • New Music: Sirrina By Hussaini Danko
      • Photos: Ali Artwork Ya Ziyarci Rahma Sadau
      • Prince Abubakar Audu Dan Takara Gwamna Jihar kogi ...
      • An Kai Hari A Garin Kauye Mafe Dake Borno
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Iran
      • Photo; Aisha Buhari, Ambode Da Bola Tinubu Wajen W...
      • Film: Download Hausa Film Shargalle Part 1
      • Al'ajabi Part 10
      • List: Makarantu Sakandare Da Suka Fi Kowani Makara...
      • Photo: Buhari Tare Da Tsohon Direban Sa Da Yar sa
      • Music: SO by Hussaini Danko
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • Zuwa Da Budurwa Yawon Duniya ( Kalli Kaci Dariya)
  • Rikicin Tsakanin Hadiza Gabon Da Zaharadeen Sani ( Bayanai Da Rahoto) S...
  • The Missing seven-year-old boy found dead in Kano
    Seven-year-old Khalifa Saminu Saleh was tragically found deceased six days after he was reported missing in the Kuruma community...
  • Sadiya Gombe Ft Al'ameen Bauchi (Ra'ayin Ki Ne Nawa) Sabuwar Waka
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Zanga-zanga A Bauchi-Gwamnatin Ta Saka Dokar Hana Fita Da Zirga-Zirga Ac...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger