1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Kazamar Gida Part 10

Kazamar Gida Part 10

By Abdul Mk
Add Comment
Tuesday, 17 November 2015
Gabansa ya fad'i da jin tambayar da Hadiyya ta watso mishi. Ya daure ya k'ak'alo 'yar dariya
"Kedai akwai ki da wasa,haba ni dan adam me zanyi da aljana ina da kamar Siyama?"
Ya fad'a cikin son maida zancen wasa. Tayi dariyar itama wanda ya taho da ruwan hawaye ta jinjina kanta zuciyarta na tururi,ta daure tace
"Sau nawa kuma akayi hakan? Kaga sai a k'ara dank'on zumunci "
Yayi dariya
"Lallai kam."
Daga haka ya bagarar da zancen kamar bai fahimci iyakar gaskiyarta take fad'a ba. Tun ba yau ba ya fahimci son da takeyi mishi hakanan bayaso ko kadan ya gaskata yanayin da yakeji game da ita.
Itama Hadiyya ganin ya share maganar ne ya sanyata yin dana sani. Tasan shikenan Jafar bazai tab'a sonta ba,daman zuciyarta ke yaudararta har ma take ganin kamar so ne yasa mu'amalarsu tayi k'arfin da har ya nemi sanin gidansu. Ashe ashe ba haka bane. Ji tayi gaba d'aya hirar ta gundureta,don haka ta katseshi da fad'in
"Bacci ya taho yaya j,zan kwanta saida safe."
Jafar shi kansa yana bukatar tunani,don haka ba musu sukayi sallama ya jona wayar a chaji. A sannu ya maida kai ya kwanta zuciyarsa cike da tunani. Hadiyya sonshi takeyi? Meyasa baiji haushinta game da hakan ba kamar yanda yakejin haushin sauran yan matan irinta masu nuna suna kaunarsa? Toh kodai shima yana sonta ne?
Ya girgiza kanshi da sauri ya k'ara muskutawa
"Bazai tab'a yiwuwa ba. Bayan Siyama babu wata d'iya mace da zan nunawa so. Babu!"
Ya fad'a a fili,cikin son kawar da tunane tunanensa,yayi addu'oinsa ya rufe ido har bacci ya daukeshi.
**********
Batayi mamakin ganin Mamanta tsaye a kanta ba saboda kukan da takeyi mai k'arfi ne. A firgice Mama ta k'araso falon ta zauna tana dubanta.
"Ladi kina cikin hayyacinki kuwa? Meke faruwa ne?"
"Bakomai mama,um...um...nayi mummunan mafarki ne."
Mama tace
"Haba Ladi shine saiki dunga kuka haka kamar ba musulma ba? Addu'a ya kamata kiyi,sannan ko menene kika gani ai iyakarsa mafarki ba wai gaske ba. Allah Yayi mana tsari da sharrukan dake cikin mafarkanmu,Ya tabbatar mana da alhairansa."
Dakyar ta iya amsawa,mama tace
"Tashi muje ki kwanta,kafin nan ki d'ora alwala"
Tabi bayan mamanta bayan ta kashe wayar ta ajiye anan kan kujera. Bata marmarin sake bud'e wannan wayar,bata da amfani tunda wanda takeso baya sonta. Ta tabbata cigaba da sauraron Jafar k'arin tashin hankali ne ga rayuwarta. Ka hak'ura da duk wanda zai nuna baya sonka,shine mafita...!
********
Kwana uku da yin haka tsakanin Jafar da Hadiyya. Ya shiga damuwa kwarai na rashin samunta a waya. Har mamakin lamarin yakeyi,toh menene kuma na damuwa har haka? Daman ai koda bata barshi yanzu ba wataran dole fa zatayi aure su rabu. Saidai wannan baisa ya bar damuwar rashin samun wayar Hadiyya ba. Gashi ko gidansu bai tab'a zuwa ba,kamar yanda ko a hoto basu san junansu ba ballantana ya sanya ran wataran zai iya had'uwa da ita.
Ita kuwa Ladi kacokam ta maida hankalinta ga karatunta duk da cewa can k'asan zuciyarta tunanin Jafar ne mamaye. Kwana ukun nan ko shago bata bin Mama suje tana fakewa da gajiyar makaranta. Babban dalilinta na gujewa shagon bai wuce fargabar yin tozali da Jafar ba,batason ganinsa ya fama mata wani mikin. Daman yanzun ma wane irin wahala ce bata sha? A kwana ukun nan gaba d'ayanta ta rame,tsananin kewar muryarsa takeyi. Saita dauko wayarta a yini fin sau goma da niyyar bud'ewa amma data tuna cewar son maso wani takeyi wanda takeso bai damu da ita ba kawai sai ta fasa. Ta koyawa kanta yawan duba darussan makarantarsu,babban takaicinta ga Basma tayi mata nisa balle ta nemi shawararta. Ita kad'ai take kid'a da rawarta. Mahaliccinta kad'ai Yasan matsalarta.
******
Ranar wata litinin ta yanke shawarar zuwa kasuwa ko don kautarwa da Mama damuwar da ta sanyawa zuciyarta akan rashin sanin dalilin chanjawarta.
Ganinta kuwa ba k'aramin farin ciki yasa Mama ba. Ladi tayi iyakar kokari wajen danne damuwarta saboda Mama. Cikin ikon Allah ma sai ya zamana a ranar ko k'eyarsa bata gani ba.
*****
Bama shagonsu Ladi ba,ko kasuwar Jafar bai lek'o shigeta da wuri ba sakamakon kiran daya samu daga Hanif,inda ya sanar dashi Siyama ta haihu da asuba anan asibiti. Farin ciki marar misaltuwa ya mamaye Jafar,cikin fad'a yace "Amma meyasa tunda aka mik'ata asibitin babu wanda ya sanarmin?"
Hanif yayi dariya
"Toh inda an sanar maka me zakayi? Ai fad'ar haihuwa yafi dad'i akan nakuda. Ka garzayo dai kaga d'anka mai kama dakai."
Jafar yayi tsalle ya sauko daga gadon. Tuni ya mance da damuwar da yake ciki na rashin jin Hadiyya.
Acan kuwa,daga Hajiya sai Amina matar Hanif ya tarar. Lokacin karfe bakwai da rabi na safe.
Jafar yayi murnar ganin Siyama da d'ansa cikin koshin lafiya. Anan waje ya zauna yayi ta kiran 'yan uwa da abokan arziki bai damu da yanda Hajiya ke kananun maganganu ba. Wai ko nauyinta baiji ba ya sungumi jaririnsa har yana sumbata.
Kafin kace me,tuni yan uwa sun cika asibitin. Hajja kanta saida tazo.
Jafar bai bar asibitin nan ba sai wajen uku na rana,saida yaci abinci yayi nak sannan ya tafi kasuwar cike da farin ciki. Ko ta kan shagonsu Mama bai bi ba,hankalinshi duka yana ga mai jego da d'ansa.
Da yamma aka sallamesu suka koma gida. Wannan yasa Jafar yana barin kasuwa bai zarce ko'ina ba sai gidansu...!!
Yakai mintuna talatin suna hira da Hanif a babban falon Hajiya,saidai babu niyyar za'ayi mishi magana da mai jego ko kuma a mik'o mishi d'ansa. Hanif yaje har wajen sau uku saidai amsar an musu wanka,tana cin abinci,ana gyarawa baby jiki. Can dai yaga abun bana k'are bane dole ya mik'e,hanif ya dubeshi
"Ba dai tafiya ba?"
Jafar yayi murmushi
"Eh zan shiga gida daganan zan wuce."
Da sauri Hanif ya mik'e
"A haba ko baby baka gani ba? Jira don Allah bari nayi musu magana."
Jafar ya koma ya zauna,yana jiyo shewar Rumaisa dasu Amina matar hanif. Hira sukeyi hankali kwance.
Hanif ya shiga ya samesu,ganin Siyama zaune kawai,yaron yana cikin gadonshi ransa ya b'aci.
"Ke wane irin iskanci ne tun d'azu mijinki yana zaman jiranki amma kin gaza fitowa? Idan ma baki da niyyar zuwa ai saiki bashi yaronsa ya gani ko?"
Siyama ta mike don daman Hajiya ce ta hanata fita tun d'azun sai fad'a takeyi ita bazata dauki rashin kunyar jafar ba,akan wane dalili zai dunga yin zarya daga haihuwa?
Ganin Hajiya batanan yasa ta fito,Hanif tuni yayi gaba da jaririn a hannu. Jafar ya karb'eshi yana dubansa,babu abunda ya bambantashi da yaron sai haske kawai da zai nuna masa. Sanyin dad'i ya mamayeshi yana jin kaunar yaron matukar gaske tana k'ara shigarsa.
"Ina wuni."
Ya d'ago ya dubeta fuskarsa dauke da murmushi
"Lafiya lau mai jego,ya jikin?"
Ta d'an yatsine fuska
"Jiki da sauki."
Ya lura tana cikin fushi,sai ya tambayeta
"Yaya dai? Akwai wata damuwa ne?"
Ta girgiza kanta har lokacin bata saki fuskarta ba
"Don Allah my j kada ka rinka zuwa akai akai,Hajiya har ta soma fad'a. Wai duka duka yaushe aka rabu a asibiti har ka biyomu? Ka bari sai mu dunga gaisawa a waya,koda ta kama zakayimin magana mai muhimmanci sai muyita a waya amma.."
Kallon da yake jifanta dashi ne ya hanata k'arasawa
"Shine dalilinki na k'in fitowa ko?"
Ya jinjina kanshi,duk wani murna da ya taho da ita da d'okin ganinta da d'ansa nan da nan ta kau. Ya mike ya mik'a mata yaron,ya sanya hannu a aljihu ya fiddo kud'i ya ajiye mata.
"Shikenan,nagode. Amma ki sani koda ban nemi ganinki ba zan nemi ganin d'ana wannan kuma babu mai hanani. Ke kam naji duk sadda kika bukaci ganina sai ki sanarmin. Amma bazan yarda da sharad'in nan ba daga haihuwa yau yau a kafamin shi. Bamai yiwuwa bane."
Ya juya ya fice rai a b'ace. Siyama taja tsaki,shi dai Jafar batasan irinshi ba. Banda zuciya babu abunda ya ajiye. Magana bata kai ta kawo ba zaiyi fushi. Ta mike ta koma d'aki.
*******
Hajja ta jefo mishi tambaya bayan ta gama lura da yanayinsa
"Kai kuma meya faru?"
Ya girgiza kai ya ja numfashi,nan ya labarta mata yanda sukayi da Siyama. Cike da mamaki Hajja tace
"Ikon Allah,daga haihuwa yau yau d'innan har an soma kafa doka? Allah dai Ya kyauta. Saika kiyaye don a zauna lafiya. Kaga kuma haihuwar fari ce,mata zasuyita zuwa saika rage shiga gidan."
Baice komai ba,Hajja ta ja shi da wata hirar game da tsarin da yayi nakai kayan barka a al'adance,
"Nikam bansan yanda kukeyi ba Hajja. Abunda yafi zan bawa anti kudad'e idan yaso sai ta had'a a mika musu."
Hajja ta gyada kanta
"Hakan yayi,Allah Ya k'ara rufa asiri."
"Amin."
*****
Bazata iya kashe kanta ba,ta lura tayi nisan da batajin kira akan sonsa. Wannan yasa tana dawowa daga shagonsu ta bud'e wayarta. Tayi mamakin jin shigowar sakonni har uku. Na farko daga kamfanin mtn ne,na biyu dana uku an turosu ne jiya da yau. Na biyun gaisuwa ce da tambayar lafiyarta daga Jafar. Na ukun kuwa,sanar da ita haihuwar Siyama yayi. Taji dad'in k'aruwar daya samu,don haka ta ajiye wayar da zummar idan ta idar da sallar isha'i zata aika mishi sakon taya murna.
Tana idarwa,mama ta lissafa kud'in adashi ta bata akan takai mata gidan hindatu mai adashi. Taji dad'in wannan aiken tasan ta samu damar siyan kati. Ta rarumi wayarta da hijabi ta fito. Saida ta soma biyawa ta sayi kati ta sanya,ta nemi gefe ta tsaya. Sak'o ta rubuta mishi ta aika sannan ta cigaba da tafiya kasancewar akwai 'yar tazara tsakaninsu da Hindatu mai adashi.
Babu dad'ewa wayarta ta soma vibrating ta duba,murmushi ya kwace mata zuciyarta na bugawa da sauri sauri. Yaushe rabonta da jin muryarsa? Da sauri ta d'aga tare da sallama.
"Deeya! Ina kika shiga ne kika manta da yaya j,bakya ko tunanin halin da zan shiga? Tabbas nayi fushi dake mai yawa."
Ta gimtse dariyarta,ta k'ara yin sallama a karo na biyu jin da tayi bai amsa na farko ba. Ya amsa mata,a hankali tace
"Yaya j,bari na isa gida zan maka flashing,yanzu ina kan hanya ne."
"OK."
Ta kashe wayar,tana mai jin wani irin farin ciki. Nan fa ta d'aga k'afarta har ta isa gidan Hajiya hindatu mai adashi. Injinsu sai aiki yakeyi,tana zaune a falon. Suka gaisa ta mik'a mata kud'in,Hajiya hindatu taji dadi,
"Shiyasa nakeson Binta,bata wasa. Takan bayar akan lokaci."
Dariya kawai Ladi tayi sannan ta tambayi Jamilah,diyarta. Ta nuna mata d'aki. Da saurinta ta nufi d'akin. Jamila tana band'aki,wannanya bata damar dannawa Jafar kira. Ko minti d'aya batayi ba ya biyo bayanta...
Uhmmm
Please like Us On   Facebook
Follow us on   Twitter


Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 14:08
In Hausa Novels
Kazamar Gida Part 10 Title : Kazamar Gida Part 10
Description : Gabansa ya fad'i da jin tambayar da Hadiyya ta watso mishi. Ya daure ya k'ak'alo 'yar dariya "Kedai akwai ki da wasa,...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Kazamar Gida Part 10"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ▼  November (308)
      • Kafin Kayi Barci
      • Yanda Ake Hada Lemon Juice
      • Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Banburaitai
      • Photos: Buhari Ya Isaa Paris Dan Halartar Taron Sa...
      • Ana Ta Samun Nasarar Kwato Shanun Sata a Kano
      • Zargin Kinshiyoyin Ta Sun Mata Asiri
      • Al'ajabi Part 16
      • Hisbah Ta Kama Wani Dan Sanda Da Yi Wa Budurwa Ciki
      • An kaiwa 'yan Shi'a hari a Masallaci a Bangaladash
      • Video: Download Highlight Leicester City 1 Manches...
      • Video: Download Highlight Barcelona 4 Real Sociedad 0
      • Yanda Ake Hada Cake
      • Photos: Yusuf da Zahra Buhari Su Halarci Taron Yay...
      • Photos: Sabin Hotuna Shahida Sanusi Lamido Sunusi
      • Buhari Ya Nada Sabun Alkalai
      • Al'ajabi Paart 15
      • Yan Boko Haram Na Shirin Kaima Abuja Hari
      • Mummunar Shiga Mai Bayyana Tsaraici Da Yan Uwa Mat...
      • New Music: Inda Rai Darabo By Hussaini Danko
      • Graphic Photos :Adadin Mutanen Da Su Ka Rasu A Har...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Atiku Abubakar
      • Graphic Photos:Yanayi Wanda Ya Kai Hari Yau A Jiha...
      • Tafsir: Rikicin Duniya Da Na Lahira By Sheikh Isa ...
      • Hanyoyin 25 Masu Sauki Domin Samun Lada Mai Yawa
      • New Music: Kana Raina By Hussaini Danko
      • Bom Ya Tashi Dan Yan Shi'a 15 A Kano
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Sarauniyar Ingila A Malta
      • Tafsir: Tambayoyi Tara Bayan Mutuwa By Sheikh Isa ...
      • Graphic Photos: Wani Dalibi Poly Ya Kashe Kansa
      • Buhari Na Neman Jefa Kasar Nan Cikin Mummunan Hali...
      • Yadda Wani Attajiri Ya Yi Wa Kansa Yankan Rago A J...
      • New Film: Zurfin Ciki 2015 Part 2 Starring Ali Nuhu
      • Yan Najeriya Sun Nuna Bacin Ransu Da Buhari
      • Dan Marigayi Audu Abubakar Ne Zai Maye Gurbin Sa A...
      • Kotu Ta Hana Wata Ma'aikaciya Sanya Hijab A Faransa
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Malta
      • Photos: An Kaddamar Da Sarkin Kano Mastayi Sabon C...
      • Photos: Gwamna Jihar Nasarawa Ya Kwanta Akan Katif...
      • Nafisah Abdullahi Tayi Allah Wadai Da Matan Da Ke ...
      • Photos: Happy Birthday Haleema Atete, Ga Sabin Hot...
      • New Film : Zurfin Ciki 2015 Part 1 Starring Ali Nu...
      • An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambia
      • Magajin Garin Kano Ya Rasu
      • Photos:Buhari,Osinbajo, Saraki, Tinubu Da Amaechi ...
      • Video: Manchester United 0 PSV 0
      • Video: Shakhtar Donesk 3 Real Madrid 4
      • Yanda Ake farfesun kifi
      • Yanda Ake Karya Sihiri Da Lalata Sharrin Aljanu
      • Photos: Buhari Ya Halarci Wajen Binne Matan Awolowo
      • Za A Fara Kama Masu Boye Fetur A Najeriya
      • Abu Ashirin Da Mata Ke So
      • Macen da Aljanna ta fi Karfin ta
      • New Music: Nayi Kira By Hussaini Danko
      • New Music : Kira Nake by Hussaini Danko
      • Yanda Ake Hada Kunu Aya
      • Al'ajabi Part 11
      • Paparoma zai je Kenya
      • An gano wata jigidar bama-bamai a Paris
      • Bangladesh ta haramta amfani da Facebook saboda Tsaro
      • Graphic Photos: Abunda Kishiyarta Ta Mata Ranar Am...
      • Hanyoyin 15 Da Zaka Bi Domin Gujewa Aikata Zinna
      • Al'ajabi Part 13
      • Al'ajabi Part 12
      • Video: Barcelona 6 Roma 1
      • Video: Arsenal 3 Dinamo Zagreb 0
      • Video: Maccabi Tel-Aviv 0-4 Chelsea
      • Photos: An Ba wa 2face Sarauta A Kaduna
      • Buhari Ya Bada Sakon Ta’aziyya Ga Iyalan Audu
      • APC Za Ta Tsayar Da Sabon Dan takara
      • New Music: Mafita By Hussaini Danko
      • New Music: Rabin Mutum By Hussaini Danko
      • Al'ajabi Part 14
      • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
      • Graphic Photos: Wata Yarinya Tana Bukatar Taimako ...
      • Hakurin Zama Da Mace Mara Biyayya
      • Photos: Aisha Buhari A Offishin FIRST LADY
      • Photos: Major AL Ayangbesan, Soja Najeriya Wanda B...
      • Boko Haram, ISIS, Al-Qaeda Na Shirin Kai Hari — Am...
      • Photos: Sabin Hotuna Iyalan Marigayi Sani Abacha
      • New Music: Shakuwa By Hussaini Danko
      • Photos: Buhari Ya Halarci Taron Kasashen Masu Arzi...
      • An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh
      • Darussa Bakwai Game Da Rasuwar Dan Takarar Gwamna...
      • Photos: Isar Buhari Iran
      • Abunda Dokar Zabe Tace Akan Mutuwar Audu
      • An yi jana'izar Abubakar Audu
      • Mutane 8 sun mutu a harin Maiduguri
      • Film: Download Hausa Shargalle Part 2 Starring Sul...
      • Photos: Adama Indimi A Sabon Hotuna
      • New Music: Sirrina By Hussaini Danko
      • Photos: Ali Artwork Ya Ziyarci Rahma Sadau
      • Prince Abubakar Audu Dan Takara Gwamna Jihar kogi ...
      • An Kai Hari A Garin Kauye Mafe Dake Borno
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Iran
      • Photo; Aisha Buhari, Ambode Da Bola Tinubu Wajen W...
      • Film: Download Hausa Film Shargalle Part 1
      • Al'ajabi Part 10
      • List: Makarantu Sakandare Da Suka Fi Kowani Makara...
      • Photo: Buhari Tare Da Tsohon Direban Sa Da Yar sa
      • Music: SO by Hussaini Danko
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • The Missing seven-year-old boy found dead in Kano
    Seven-year-old Khalifa Saminu Saleh was tragically found deceased six days after he was reported missing in the Kuruma community...
  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Rikicin Tsakanin Hadiza Gabon Da Zaharadeen Sani ( Bayanai Da Rahoto) S...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger