1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Kazamaar Gida Part 3

Kazamaar Gida Part 3

By Abdul Mk
Add Comment
Tuesday, 3 November 2015
Kwana biyu da yin haka,babu laifi Jafar yaga chanji domin yakan dawo ya tarar an share gidan. Hakanan dakunanta tun gyaran da yayi musu har lokacin bata b'ata ba amma sunyi k'ura saboda iskar ruwa da ake yawan yi. Bai ce mata komai ba ya bita a hakan. Ai da dai wannan shegen kazantar ya gwammace suyita tafiya hakanan da kansa ya dunga gyara inda baiyimishi ba.
*************
Tun ranar da Jafar yak'i waiwayar shagon take cikin damuwa. Ta rasa abunda yake yi mata dadi. Tana jin kanta a mai laifi,inama bata nemi sanin matsalar Jafar ba. Yanzu gashinan ya kauracewa shagon nasu duk da batasan dalilinsa ba saidai kwarai tana zargin kanta. Gashi har Mama ta dawo,rashin ganinsa baisa ta matsa da tambaya ba tunda a yanzu mijin aure ne. Saidai tana mamakin yanda bai zuwa su gaisa kamar yanda a baya yakan yi koda bazai ci abincinsu ba. Ladi ai ta fita shiga damuwa domin sau biyu tana zuwa nemansa a shago don mik'a mishi sauran chanjinsa amma bata samunshi.
Babu zato babu tsammani,ta shigo sanye da kayan makaranta wanda aka dinka hijibin har gwuiwa,ta hangoshi zaune a shagon yana cin abinci yana hira da Mama hankali kwance. Nan da nan ta sauke ajiyar zuciya,da saurinta ta k'araso ciki da sallama. Sai a sannan ne Jafar yasan da shigowarta,murmushi yayi mata
"'Yar nijar."
Tayi dariyar farin cikin ganinsa,Jafar yana burgeta sosai saboda mutuncinsa. K'arasawa tayi ta gaisheshi a ladabce ya amsa cikin sakin fuska. Ta juya ga sauran customers nasu ta gaishesu sannan ta maido dubanta ga Jafar
"Yayana nayi zaton fushi kakeyi dani,don Allah idan maganata ta rannan ta b'ata ranka kayi hakuri. Da ace nasan bazakaji dad'inta ba,bazan yi ba."
Jafar ya girgiza kansa
"Baki b'atamin rai ba Ladi,saidai wasu dalilaina ne suka sanya nabar lek'owa. Kiyi hakuri,ki bar zargin kanki. Ai ke Ladi baki da wata d'abi'a da zaki b'ata ran mutum dashi,kina da kaifin basira da hankali. Uwa uba gaki mai tsafta wanda.."
Ya sanyawa bakinsa linzami,idan baiyi takatsantsan ba yanzu sai yayi furucin da Ladi zata d'ago damuwarsa. Don haka ya share batun yana murmushi
"Ke dai kada ki damu kanki,bakiyi laifi ba kinji ko?"
Murmushinta ya fad'ad'u har ana hangen hak'oranta
"Nagode yayana,bari na barka ka kammala sannan kada kace zaka biya fa. Har yanzu chanjinka suna...." Ya katseta da hanzari
"Na bar maki 'yar nijar. Ki rik'esu ki siya powder."
Sukayi dariya,tayi gaba bayan tayi mishi godiya. Ranar kam zuciyarta fes.
*********
Da misalin hudu da rabi na yammacin ranar juma'a,Jafar yana tare da abokansa na kasuwa suna ta hira da shek'a dariya. Idan suka sami customers kuma sai hankalinsu ya koma garesu.
Ibrahim ne ya katseshi
"Kaifa tun dazu wayarka tana ringing."
Ya mike da sauri ya shiga shagon ya zaro wayar daga chaji zuciyarsa babu ko d'igon damuwa,saidai ganin lambar Rumaisa duk sai ransa ya b'aci. Duk a yayyun Siyama babu wacce jininsu bai hadu ba kamar ta. Itace kan gaba wajen yiwa matarsa hud'ubar rashin arziki,domin da kunnensa yasha jinsu a falo yayinda suke hira. Ba'ason ransa ba ya dauka,kafin yakai ga magana ta rigashi
"Haba Jafar,kasan sau nawa nake ta danna maka kira ne? Wannan bayi bane,saika dunga ajiye waya a kusa tunda dai kabar gidanka ba lafiya."
Nan take gabanshi ya fadi
"Kiyi hakuri anti,wayar na sanyata chaji ne. Meke faruwa a gidan nawa?"
Ai saita soma fad'a
"Lallai Jafar,wannan ya nuna baka kula da Siyama. Banda haka ace tun safe matarka take fama da jikinta baka da masaniya? Toh Allah Ya kyauta,idan kaga dama kazo ka samemu muna nan a asibitin Getwell har Hajiya."
Ai bai jira komai ba ya mike yana maida hularsa,ya dubi ibrahim
"Zan tafi asibiti ne madam babu lafiya,koda Alhaji yayi kiranka please ka sanar dashi."
Daga haka ya fice,abokansa suna tambayar lafiya saidai bai iya basu amsa ba.
Yana tuk'a mashin d'insa yana tunanin Siyama. Daman fa tun safe da ya nemi hakkinsa ta gudu daga d'akin zuwa nata,acewarta bacci takeji sosai. Hakan yasa ta k'ular dashi don hatta kud'in cefanan anan kan kujera ya ajiye mata. Yayi dana sanin biyewa mace,inama alokacin ya cusa kansa har d'akin domin bincikar lafiyarta. Duk da d'abi'un Siyama fa yana sonta sosai wannan ne babban dalilin hakurin da yake da ita.
Yana tunane tunanensa yana tuk'i har ya iso k'ofar asibitin ya faka.
Ko ciwon me siyama takeyi..?
Kai tsaye ya shiga asibitin,duk iya waige waigensa bai hangosu zaune ba. Wannan ya sanyashi fiddo wayarsa ya dannawa rumaisa kira. Bayan ta dauka ya nemi sanin inda suke. Lek'owa tayi,ya hangota ta fito daga hannun hagunsa. Fuskarta a daure,suna hada ido ta watsa mishi kallon banza sannan tayi gaba. Har zuciyarsa baiji dadin hakan ba dolensa ya hadiye sanin da yayi ta d'arashi a shekaru babu yanda ya iya mata.
Zaune ya iske Hajiya,mahaifiyar Siyama. Siyama tana kwance akan cinyarta. Ya k'arasa cikin ladabi ya durkusa yana gaisheta. Hajiya bata ko kalleshi ba ta amsa a ciki
"Lafiya."
Bai wani damu ba daman tun a baya Hajiya ba son aurensa da Siyama takeyi ba,kwarai taso 'yarta da auren d'aya daga cikin yaran masu hannu da shunin dake rububinta. Saidai Allah Yafi gaban haka,aure kuma kaddararSa ce. Ko bayan haka ma soyayyarsa da Siyama da kuma karfin zumuncin dake tsakanin iyayensu maza bana wasa bane.
Jafar dakyar ya iya yin tambayarsa
"Yaya jikin nata?"
Kamar jira Rumaisa takeyi,tayi saurin cafewa
"Bakinka baiji kunyar tambayar...."
"Kiyimin shiru,baki ganin a inda muke ne?"
Maganar Hajiya tasa Rumaisa hadiye sauran zancen tana mai kwafa. Kafin waninsu ya samu damar cewa wani abu,wani ma'aikacin asibitin ya fito daga dakin da suke fuskanta,suka maida hankali gareshi yayinda ya mik'owa Rumaisa takarda
"Ga result saiku mik'awa Doctor."
Tayi godiya,fuu ta wuce,Hajiya na biye da ita rike da hannun Siyama. Jafar baiyi k'asa a gwuiwa ba ya mara musu baya saboda yasan rashin binsu ma wata matsalar ce. Tausayin Siyama duk yabi ya rufeshi,har lokacin tunanin abunda ya faru gareta yakeyi saidai bai iya tsinkayar komai ba. Bayan likita ta kammala duba result ta d'ago tana murmushi tace
"Na tayaku murna She's pregnant."
Dam! Tamkar an soki kirjin Jafar,jin da yayi jiri yana son kwasarsa ne ya sanya babu shiri ya zube kan kujera. Allah shaida ba'a bakin cikin samun ciki na sunnah amma shi kam yaji. Yana son Siyama,yana son haihuwa saidai hankalinsa yayi mugun tashi jin cewar ciki ne da ita. Yanzun ma ya aka k'are da kazantar ta balle kuma har a samu rabon d'a? Ai fa saidai Allah Ya sassauta.
"Jafar bakaji abunda akace bane?"
Rumaisa wacce tun furucin likita ta zubo masa na mujiya domin jin abunda zaice ta katse tunaninsa. Ya d'ago kansa da sauri yana washe baki wanda ba don Allah bane,
"Naji Anti,farin ciki ne ya hanani magana."
Sai kuma ya tuno da Hajiya a wajen. Doctor ta dubesu bayan kammala rubuce rubucenta
"Oh wannan ne mijin nata?"
Har lokacin bai rufe bakinsa ba
"Eh nine."
Ta gyada kai tana murmushi
"Congrats."
"Thank you."
Ta miko musu file
"Sai a siya mata wadannan magunguna. Sannan itama ta dunga kula da kanta sosai. Ta kiyaye k'aidar shan magani. Allah Ya raba lafiya."
Sukayi godiya suka fito. Ya saci kallon Siyama,murmushita sakar mishi har baisan lokacin daya maida martani ba da nasa murmushin wanda ke had'uwa da zuciyarsa su k'ara masa wani d'aci. Yakai dubansa ga Rumaisa
"Anti kawo a amso magungunan."
Ta mik'a mishi su kuma sukayi waje.
Ya kammala ya fito ya iskesu cikin motar Rumaisa,magana sukeyi amma zuwansa ne yasa su yin shiru har saida yakai ga tsarguwa.
Ya mik'awa Rumaisa magungunan,ta karb'a a wulakance.
"Jafar."
Da sauri ya russuna
"Na'am Hajiya."
"Inaso nasan irin zaman da kakeyi da Siyama,nayi mamakin yanda muka je gidan da niyyar ziyartarta saidai muka isketa kwance cikin amai,gaba dayanta kaca kaca. Wane irin zama ne da har matarka bata da lafiya tun safe amma ace har ka iya sanya k'afa...."
"A'a fa Hajiya,wallahi bai sani..."
Cikin zafin nama Anti rumaisa ta kaiwa bakin Siyama bugu. A fusace Hajiya tace
"Shashashar banza kawai,ana nema mata 'yancinta 'yar iskar yarinya tak'i ganewa. Don ubanki inace ke da bakinki kika sanar damu tun bai fita ba kike a wannan yanayin? Shine salon ki maidamu yan iska kike shirin k'aryatawa?"
Gama maganar Hajiya,ta maida dubanta ga Jafar wanda haushi ya isheshi,yanda yakejin zuciyarsa inda ace ba mahaifiya take ga Siyama ba, da babu abunda zai hanashi barin wajen.
"Kaga Jafar,ba ni daka raina ba,ko Alhaji mahaifi ga siyaman da kake tak'ama shine jinin Alhaji Rilwan(mahaifinsa.),bazai yarda da wulakanci ba a aure. Don haka tun wuri ka chanja takunka don muddin ka cigaba da tafiya haka zan fito fili na nuna maka dagaske nake bani kaunar aurenka da Siyama. Ja motar mu tafi."
Ta k'arashe tana mayar da dubanta ga Rumaisa. Rumaisa da zuciyarta tayi fes da wannan wankin da Jafar yasha a wajen Hajiyarsu,ta gyara zama ta rufe k'ofa. Mik'ewa yayi har lokacin bai samu damar cewa uffan ba,yana duban yanda Siyama tayi wani rau rau da ido,Rumaisa ta figi motar ta saitata suka fice daga asibitin.
Ransa ya b'aci ba kad'an ba,wai me Hajiya da Rumaisa suke nufi dashi ne? Yasan Hajiya tun farko bata kaunar aurenshi da Siyama wannan kad'ai ya isa ya janyo mishi tsana a wajenta. Toh ita waccan uwar shishshigin baisan layin da zai ajiyeta ba,ko ita d'inma tana bayan Hajiyar ne,oho.
Cikin fusata Jafar ya bar asibitin bai dire ko'ina ba sai k'ofar gidan mahaifinsa.
Barka da kwana..!
Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 14:44
In Hausa Novels
Title : Kazamaar Gida Part 3
Description : Kwana biyu da yin haka,babu laifi Jafar yaga chanji domin yakan dawo ya tarar an share gidan. Hakanan dakunanta tun gyaran da yayi musu ha...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Kazamaar Gida Part 3"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ▼  November (308)
      • Kafin Kayi Barci
      • Yanda Ake Hada Lemon Juice
      • Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Banburaitai
      • Photos: Buhari Ya Isaa Paris Dan Halartar Taron Sa...
      • Ana Ta Samun Nasarar Kwato Shanun Sata a Kano
      • Zargin Kinshiyoyin Ta Sun Mata Asiri
      • Al'ajabi Part 16
      • Hisbah Ta Kama Wani Dan Sanda Da Yi Wa Budurwa Ciki
      • An kaiwa 'yan Shi'a hari a Masallaci a Bangaladash
      • Video: Download Highlight Leicester City 1 Manches...
      • Video: Download Highlight Barcelona 4 Real Sociedad 0
      • Yanda Ake Hada Cake
      • Photos: Yusuf da Zahra Buhari Su Halarci Taron Yay...
      • Photos: Sabin Hotuna Shahida Sanusi Lamido Sunusi
      • Buhari Ya Nada Sabun Alkalai
      • Al'ajabi Paart 15
      • Yan Boko Haram Na Shirin Kaima Abuja Hari
      • Mummunar Shiga Mai Bayyana Tsaraici Da Yan Uwa Mat...
      • New Music: Inda Rai Darabo By Hussaini Danko
      • Graphic Photos :Adadin Mutanen Da Su Ka Rasu A Har...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Atiku Abubakar
      • Graphic Photos:Yanayi Wanda Ya Kai Hari Yau A Jiha...
      • Tafsir: Rikicin Duniya Da Na Lahira By Sheikh Isa ...
      • Hanyoyin 25 Masu Sauki Domin Samun Lada Mai Yawa
      • New Music: Kana Raina By Hussaini Danko
      • Bom Ya Tashi Dan Yan Shi'a 15 A Kano
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Sarauniyar Ingila A Malta
      • Tafsir: Tambayoyi Tara Bayan Mutuwa By Sheikh Isa ...
      • Graphic Photos: Wani Dalibi Poly Ya Kashe Kansa
      • Buhari Na Neman Jefa Kasar Nan Cikin Mummunan Hali...
      • Yadda Wani Attajiri Ya Yi Wa Kansa Yankan Rago A J...
      • New Film: Zurfin Ciki 2015 Part 2 Starring Ali Nuhu
      • Yan Najeriya Sun Nuna Bacin Ransu Da Buhari
      • Dan Marigayi Audu Abubakar Ne Zai Maye Gurbin Sa A...
      • Kotu Ta Hana Wata Ma'aikaciya Sanya Hijab A Faransa
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Malta
      • Photos: An Kaddamar Da Sarkin Kano Mastayi Sabon C...
      • Photos: Gwamna Jihar Nasarawa Ya Kwanta Akan Katif...
      • Nafisah Abdullahi Tayi Allah Wadai Da Matan Da Ke ...
      • Photos: Happy Birthday Haleema Atete, Ga Sabin Hot...
      • New Film : Zurfin Ciki 2015 Part 1 Starring Ali Nu...
      • An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambia
      • Magajin Garin Kano Ya Rasu
      • Photos:Buhari,Osinbajo, Saraki, Tinubu Da Amaechi ...
      • Video: Manchester United 0 PSV 0
      • Video: Shakhtar Donesk 3 Real Madrid 4
      • Yanda Ake farfesun kifi
      • Yanda Ake Karya Sihiri Da Lalata Sharrin Aljanu
      • Photos: Buhari Ya Halarci Wajen Binne Matan Awolowo
      • Za A Fara Kama Masu Boye Fetur A Najeriya
      • Abu Ashirin Da Mata Ke So
      • Macen da Aljanna ta fi Karfin ta
      • New Music: Nayi Kira By Hussaini Danko
      • New Music : Kira Nake by Hussaini Danko
      • Yanda Ake Hada Kunu Aya
      • Al'ajabi Part 11
      • Paparoma zai je Kenya
      • An gano wata jigidar bama-bamai a Paris
      • Bangladesh ta haramta amfani da Facebook saboda Tsaro
      • Graphic Photos: Abunda Kishiyarta Ta Mata Ranar Am...
      • Hanyoyin 15 Da Zaka Bi Domin Gujewa Aikata Zinna
      • Al'ajabi Part 13
      • Al'ajabi Part 12
      • Video: Barcelona 6 Roma 1
      • Video: Arsenal 3 Dinamo Zagreb 0
      • Video: Maccabi Tel-Aviv 0-4 Chelsea
      • Photos: An Ba wa 2face Sarauta A Kaduna
      • Buhari Ya Bada Sakon Ta’aziyya Ga Iyalan Audu
      • APC Za Ta Tsayar Da Sabon Dan takara
      • New Music: Mafita By Hussaini Danko
      • New Music: Rabin Mutum By Hussaini Danko
      • Al'ajabi Part 14
      • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
      • Graphic Photos: Wata Yarinya Tana Bukatar Taimako ...
      • Hakurin Zama Da Mace Mara Biyayya
      • Photos: Aisha Buhari A Offishin FIRST LADY
      • Photos: Major AL Ayangbesan, Soja Najeriya Wanda B...
      • Boko Haram, ISIS, Al-Qaeda Na Shirin Kai Hari — Am...
      • Photos: Sabin Hotuna Iyalan Marigayi Sani Abacha
      • New Music: Shakuwa By Hussaini Danko
      • Photos: Buhari Ya Halarci Taron Kasashen Masu Arzi...
      • An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh
      • Darussa Bakwai Game Da Rasuwar Dan Takarar Gwamna...
      • Photos: Isar Buhari Iran
      • Abunda Dokar Zabe Tace Akan Mutuwar Audu
      • An yi jana'izar Abubakar Audu
      • Mutane 8 sun mutu a harin Maiduguri
      • Film: Download Hausa Shargalle Part 2 Starring Sul...
      • Photos: Adama Indimi A Sabon Hotuna
      • New Music: Sirrina By Hussaini Danko
      • Photos: Ali Artwork Ya Ziyarci Rahma Sadau
      • Prince Abubakar Audu Dan Takara Gwamna Jihar kogi ...
      • An Kai Hari A Garin Kauye Mafe Dake Borno
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Iran
      • Photo; Aisha Buhari, Ambode Da Bola Tinubu Wajen W...
      • Film: Download Hausa Film Shargalle Part 1
      • Al'ajabi Part 10
      • List: Makarantu Sakandare Da Suka Fi Kowani Makara...
      • Photo: Buhari Tare Da Tsohon Direban Sa Da Yar sa
      • Music: SO by Hussaini Danko
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...
  • Yadda Kotu Ta Daure Bobrisky Watanni Shida Ba Tare Da Zabin Biyan Tara Ba
    Kotu ta daure Bobrisky watanni 6 ba tare da zabin biyan tara ba Babbar kotu a jihar Lagos ta yanke hukunci ga Idris Okuneye da a...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger