1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Al'ajabi Part 6

Al'ajabi Part 6

By Abdul Mk
Add Comment
Wednesday, 18 November 2015
MUM ta dade tana kallona cikin takaici jim kadan tace " Me tayi miki kika mareta??"
Na koma kan kujera na zauna nace " zuwa... tayi ta giftani ina kallo ta kare min ban gani ba kuma tambayarta tayi min shiru."
ta kada kai tace " lallai humaira rashin mutuncin naki yakai, kawai daga na kirata ta gifta ta gabanki shine abin duka??"
Na zunburo baki nace mum " kare min fa tayi kuma......."
Ta katse ni da cewa " ke dalla can rufa mana baki kice kawai wulakancinki ya motsa to kin daketa kinji dadi, idan kinfi karfinta ai akwai Allah."
Ta nufi inda hanne ke zaune har yanzu bata tashi ba sai kuka da take yi.
Na dan kara bata rai tare da gyara zama nace " ni mum wlh bakya yimin adalci a komai ba zaki taba goyon bayana ba kullum nice me laifi a wurinki akan wadannan banzayen."
Nakai karshen maganar da kauda kai.
Mum tace " anki a goya miki bayan wace gsky gareki?? Ke ko kunya baki ji ba don Allah?? ki rasa wacce zaki zage kwanjinki akanta sai yar aikin gdnku wadanda yakamata ace kin jasu a jikinki ki nuna musu kauna."
Na kalli hanne na zabga mata harara nace " wadannan shashashan matsiyatan zanja a jikina?? Allah ya kiyaye.
Mum tace " to tunda ba zaki kyalesu susha iska ba ba ruwanki dasu basu shiga rayuwarki ba kada ki kara shiga tasu idan kuma kika ku wlh zan basu dama idan kika dakesu su rama suyi miki dan banzan duka ai ba karfinsu kika fi ba. Taja hannunta suka wuce, nabi mum da kallon mamakin jin abinda ita kanta tasan bazai yiwu ba, nace " Su dakeni fa kika ce?? "
Ta juyo da sauri tace " Eh don ubanki ".
Nabita da kallo ganin abin ya dau zafi da yawa ta juya suka bar falon da nake a zaune.
Na gyara zama na hade rai nayi kicin-kicin kamar na fashe da kuka, wai ni ake zagi akan wannan banzar yar aikin? lallai zamanta yazo karshe a gidan nan bari dady ya dawo.
BAYAN AWA DAYA naji motsin dawowar dadyna na kakalo sabon fushi da takaici, dady yana shigowa yayi ido hudu dani cikin fushi, yayi saurin ajiye jakarsa tare da tunkaro inda nake zaune " my daughter ( daya daga cikin sunayen da yake kirana dasu ) menene ya faru haka? waye ya taba min ke?"
Nayi shiru na kara hade rai kawai na juyar da kaina.
Dady ya zauna gaf dani cikin kasa-kasa da murya yace " fada min mana waye ya taba ki? uhummm?"
Cikin shagwaba na mirgina kai nace " ba mum bace......."
Me kuma tayi miki??
Ya tambaya da sauri.
nace " wai..... zata sa yan aiki su rinka dukana "
dady har wani dan babban motsi yayi tare da mai-maita abinda na fada " su dakeki??".
na gyada kai.
Ya juya da sauri ya fara kwallawa mum kira.
Hajiya!!!!! Hajiya!!!!!
Da saurinta ta fito izuwa falon da faddady yace " Me yasa kika batawa humaira rai, wai ke hajiya me yasa kike haka ne don Allah.... to to yanzu me kike nufi yar aiki tafi yar da kika haifa da cikinki kenan??"
Mum ta tabe baki tace " au wai da akan wannan ne kake kwala min kira haka sai kace wani tashin hankali??"
Au kina nufin shi wannan ba komai bane kenan?? kinga hajiya ran kowa zai baci a gidan nan fa.
Mum tace " rainin nata ne yayi yawa nace zansa a dai daita mata zama.
Na tsandara ihu nace kaji ko dady??
Dady ya kara rudewa ya fara zabga bala'i ta inda ya shiga batanan yake shiga ba.
Zuwa can nace " dady kawai a kori yan aikin nan dukansu ".
dady ya juyo yace " kwantar da hankalinki, abinda za'ai kenan suna ina ne??"
Mum tace " Wai suwa za'a kora?? bazai yiwu ba sbd duk cikinku ba wadda kuka dauka kuma baku kuke biyansu ba nice don haka babu me korar minsu ina jin dadin aiki dasu......
Munji tafi kici gaba da harkokinki kada ranmu ya baci duka, Allah ya baka hakuri.
Ta juya ta nufi sashinta, dady ya juyo gareni ya fara rarrashina ni kuwa sai wani kara hade rai nake.
Kinga manta dasu kinji humaira na, ba wanda ya isa ya taba ki duk wanda ya kara bata miki rai wlh tamuce ni dashi.
Kada ki manta fa gobe iwar haka kina kasar birtaniya kin bar musu kucakar kasar tasu zaki fara rayuwa cikin turawa ba wanda zai takura miki inda iskar da zaki shaka ma ba irin wannan bace.
Jin hakan da nayi yasa nadan saki raina kadan, yace " to danyi murmushi mana "
Na saki rai sosai yace " Yauwa ko ke fa! gobe kiyi kokari ki tashi da wuri sbd jirginki na safe ne an gama duk wasu shirye-shirye kina zuwa direct zaku daga shuuuuu!!! sai london."
yakai maganar da murmushi.
Na dan tabe baki cikin shagwaba nace " dady nifa dakai zamu tafi idan muka je sai ka dawo."
Ya dubeni yace " to ke banda abinki ina naga lokacin binki har london kuma na dawo? kedai karki damu jirgin na musamman ne zaki samu duk abinda kike bukata kuma za'a kula daku sosai musamman ma ke yar lele.
Nayi murmushi kawai.
Daddy ya mike ya dau jakarsa bari na shiga ciki ko?
"To dady" Na fada idona na kasa ya wuce.
Na daga kaina na dubi katafaren agogon dake manne a jikin bango karfe 6:15pm sallar magaribar ma ai da saura na mayar da kaina ga t.v din naci gaba da kallo.
$$$$$$$$$$$$
in Alhaji lfy irin wanWashe gari misalin karfe 8:00am na safe zaune muke mu uku, mum da dady na zaune a kujeru daf da juna yayinda nake zaune a kujerar dake fuskantarsu.
faffadan tebirine a gabanmu kayan abinci kala-kala jere bisa kansa wadanda suka dace da karin safe, babu wanda ke magana a cikinmu.
Humaira!!!!!!!!!!!!!
dady ya kira sunana, na dago a hankali na dubeshi.
yace " misalin 11:30 na safen nan zaku tashi, abinda nake so dake shine kibi a hankali kuma ki kula sosai sbd kasar da zaki je ba taki bace ba wadda kike ciki bace kuma ba wadda kika saba da ita bace, kiyi abinda yakai ki kawai shine karatu ki samo abinda zanyi alfahari dashi sbd ina da comfidence 100% akanki kuma ba zaki bani ba.
Insha-Allahu dady. Na fada tare da mayar da kaina ga kofin tea dake hannuna.
Daddy ya mike yace " bari inje na shirya na fita ina da meeting karfe tara hajiya ina takardun nan dana baki ajiyansu jiya??
Ta dago kai a karon farko tace " Suna nan cikin lokar sama." Ok " ya fada tare da dubana yace " yar lele na Allah ya kiyaye hanya, da zarar kun sauka zanyo miki waya."
To dady na fada ya juya nudi dakinsa.
Na mike na koma kan kujerar dake gaf da mum nace " Momina banji kince komai ba."
To me zance???
Ta fada kanta na duban abinda take ci.
Nace yakamata kice wani abu saboda kinga tafiya zanyi ta shekaru da yawa kodai bakin cikin rabuwa dani kike yi da yawa haka har ya hana ki magana??"
A'A ta fada tare da cewa " nifa haushinki kawai nake ji "
Na bita da kallo lokaci guda nayi yar gajeriyar dariya nace " da gaske??"
ta gyada kai kawai.
Na kwantar da kaina a jikinta nace " sorry my mum ai nasan da wasa kike ba zaki taba jin haushi na ba, uhmm! mum pls sarkar nan don Allah ki bani zanyi amfani da ita acan.
Ta girgiza kai tace " kefa kika nuna halin ko in kula da ita sai yanzu zaki ce kina so??"
Mum dama can ina sonta wlh zan kula da ita, Zaki bani??
nakai karshen maganar da kwantar da murya.
Mum ta dubeni kadan ta kauda kai tace " Zan baki ".
Na saki fuska hade da alamar jinjina nace " Thank you MUM bari naje na fara shiri. "
Na nufi dakina.
Misalin karfe goma 10:00am mufida tazo kawowa momi sako ta iske ina gaf da gama shirina ta tayani muka karasa na tilasta mata ta tsaya don yimin rakiya izuwa airport.
MUFIDA y'a ce a wurin haj. jameela kawar mum kuma aminiyarta, mufida ce kadai zan iya cewa kawata a duniya don da ita kawai na yarda muyi kawance sbd ta wasu bangarorin halinmu yazo daya duk da muna da banbanci da ita sosai a wasu bangarorin.
Misalin karfe 10:15am Nayi sallama da momi da sauran wadanda zan iya sallama dasu sauran yan aikin gidanmu kuwa da rashin mutunci muka rabu don ban hakura ba sai da nayi final.
A jibgegiyar mota kirar PRADO muka fito, mufida na gefena sai kuma mutum biyu har direba dake gaba.
Mukanyi hira jefi-jefi da mufida, kaina sai wani kumbura yake waini zani kasar turai.
Cikin kankanin lokaci muka isa AMINU KANO international airport, tunda naga jirgin dazai daga damu na yarda bana yara bane saboda haduwarsa, ya isa a nunashi a ko'ina.
Ban dauki lokaci ba aka gama tantanceni na juyo na karbi jakunkuna na mukai sallama da mufida...
****************************
Shigata jirgin ya tabbatar min da abinda dadyna ya fada, tsaruwarsa daga ciki yafi yadda nake ganinsa daga waje domin ya wuce duk yadda nake tsammani.
kai tsaye sit dina na wuce na zauna duk da cewa yaune karon farko dana shiga jirgi irin wannan amma ban yarda na nuna hakan ba don kada wadanda ke cikin jirgin su raina ni.
Abinda na lura dashi shine kowa naji da kansa a cikin jirgin sbd daga manyan attajirai masu tafiya kasuwanci sai yayan attajirai masu zuwa karatu irina, babu ma zaton samun dan talaka a ciki bare a samu din. Kamar yadda aka shirya 11:00am dai dai jirgin ya daga kai tsaye izuwa birnin london tafiya mafi tsawo dana fara yi a rayuwata, jami‘an cikin jirgin kuwa sai nan nan ake damu duk abinda muka bukata ba bata lkc ake bamu.
Awanni nata shudewa 2n ina sha‘awar tafiyar har sai dana gaji amma bamu iso ba, duk na kosa sbd wannan ne karon farko dana taba yin tafiya irin wannan daga karshe madai wani nannauyan barci ne ya kwashe ni ban farka ba sai AIRPORT na birnin londôn, A hankali daya bayan daya muka sakko daga cikin jirgin.
wowwww!!! Nan fa naga abin mamaki domin ba birnin ba airport din kadai abin kallo ne ban taba tsammanin akwai wuri me kyau da kawatuwa irin wannan lallai duk yadda ake bada lbrn birnin nan ya wuce nan, duk yadda nakai da ji da kai sai dana zama kamar wata yar kauye a wurin.
saukowarmu keda wuya jami‘an filin jirgin suka yo kanmu nan fa aka shiga secreening kala-kala harda wanda ban taba ji ba ko a lbr, bayan na cika duk wani sharadine aka bani damar ficewa daga airport din, ban jima ba kuwa wata jibgegiyar mota me matukar fadi da tsawo ta iso like take da banner din OXFORD UNIVERSITY bamu dauki tsawon lokaci ba ta debemu tare da mutane daban-daban da muka zo daga wurare da kasashe maban-banta, Anan ne fa naji kwalta tamkar ita ta shimfida kanta, duk inda motar tabi titine luwai-luwai ba gargada bare rami.
Shuuuuuuu!!!!! A haka motar ke tafiya tamkar jirgin sama ban-bancin kawai ita wannan a kasa take tafiya ba‘a sama ba.
Gefe guda tsarin gine-ginen birnin wanda keda matukar tsayi tamkar zasu tabo can kololuwar sama sun kawatar dani matuka.
gashi kowa irin rayuwar da nafi so yake yi ta ba ruwan kowa da wani, kowa ka gani harkar gabansa yakeyi. jim kadan muka iso katafariyar jami‘ar daya daga cikin mafi girma, daukaka da suna a duniya, bayan komai ya kammalu kuma kai tsaye aka yimin jagora izuwa masaukina.
Ni kadai ce a sashin nawa wanda ya kunshi duk abubuwan da nake bukata.
************************* Nan fa na shiga karatu gadan-gadan kasancewarsa wajene da ko baka so sai kayi karatu, da farko na dauka a nigeria ne naci gaba da jiji dakai da takama sai naga ina!! domin a banza wajene da kowa keji da duk abinda nake ji dashi shima. Dole tasa na sakko na fara maraba da kowa nan da nan kuwa na tara kawaye masu yawan gaske tamkar bani ba, na saki jiki da mutane sosai. Da yake ba karatu ne irinna na nigeria ba cikin shekaru biyu kacal na kammala degree na na farko a hakan ma don mun sami dan tsaiko ina daya daga cikin wadanda suka sami sakamako me kyan gaske hakan yasa makarantar ta bani damar yin masters degree kyauta kasancewar ina jin dadin zaman yasa na amince na zarce cikin ba tare da jinkiri ba. shekara daya kuma na kammala masters, degree biyu cikin shekaru uku kacal, wannan shine tarihin kara2na da yadda na samu masters degree a kasar birtaniya.
“hmmm..... Lallai gskyr Bahaushe da yace ‘Talaka bawan Allah‘ domin talakan nigeria ne zai kwashe shekaru hudu yana neman diplomer bai samu ba“
Ahmad ya fada sanda ya kauda kansa daga kan littafin lkc guda ya mayar da kansa ya dora. kammaluwar komai tasa na tattaro inawa-inawa nayo nigeria, ranar laraba misalin 12:00pm jirginmu yayo nigeria.
dirarmu keda wuya dady ya iso tare da wasu daga cikin yaransa aka daukeni direct mukai gida, nan fa girman kai, takama, gadara da raina mutane ya dawo sabo fil. Na fara jin nifa yanzu nafi kowa kuma samun kamar ni sai an tona kai zaiyi wuya ma a samu mace kamar ni da tattara abubuwan da nake dasu.....
Hmmm'un yanxu akapara shirin..!
BARKAN KU DA ASUBAH..!
Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 13:13
In Hausa Novels
Title : Al'ajabi Part 6
Description : MUM ta dade tana kallona cikin takaici jim kadan tace " Me tayi miki kika mareta??" Na koma kan kujera na zauna nace " zu...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Al'ajabi Part 6"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ▼  November (308)
      • Kafin Kayi Barci
      • Yanda Ake Hada Lemon Juice
      • Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Banburaitai
      • Photos: Buhari Ya Isaa Paris Dan Halartar Taron Sa...
      • Ana Ta Samun Nasarar Kwato Shanun Sata a Kano
      • Zargin Kinshiyoyin Ta Sun Mata Asiri
      • Al'ajabi Part 16
      • Hisbah Ta Kama Wani Dan Sanda Da Yi Wa Budurwa Ciki
      • An kaiwa 'yan Shi'a hari a Masallaci a Bangaladash
      • Video: Download Highlight Leicester City 1 Manches...
      • Video: Download Highlight Barcelona 4 Real Sociedad 0
      • Yanda Ake Hada Cake
      • Photos: Yusuf da Zahra Buhari Su Halarci Taron Yay...
      • Photos: Sabin Hotuna Shahida Sanusi Lamido Sunusi
      • Buhari Ya Nada Sabun Alkalai
      • Al'ajabi Paart 15
      • Yan Boko Haram Na Shirin Kaima Abuja Hari
      • Mummunar Shiga Mai Bayyana Tsaraici Da Yan Uwa Mat...
      • New Music: Inda Rai Darabo By Hussaini Danko
      • Graphic Photos :Adadin Mutanen Da Su Ka Rasu A Har...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Atiku Abubakar
      • Graphic Photos:Yanayi Wanda Ya Kai Hari Yau A Jiha...
      • Tafsir: Rikicin Duniya Da Na Lahira By Sheikh Isa ...
      • Hanyoyin 25 Masu Sauki Domin Samun Lada Mai Yawa
      • New Music: Kana Raina By Hussaini Danko
      • Bom Ya Tashi Dan Yan Shi'a 15 A Kano
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Sarauniyar Ingila A Malta
      • Tafsir: Tambayoyi Tara Bayan Mutuwa By Sheikh Isa ...
      • Graphic Photos: Wani Dalibi Poly Ya Kashe Kansa
      • Buhari Na Neman Jefa Kasar Nan Cikin Mummunan Hali...
      • Yadda Wani Attajiri Ya Yi Wa Kansa Yankan Rago A J...
      • New Film: Zurfin Ciki 2015 Part 2 Starring Ali Nuhu
      • Yan Najeriya Sun Nuna Bacin Ransu Da Buhari
      • Dan Marigayi Audu Abubakar Ne Zai Maye Gurbin Sa A...
      • Kotu Ta Hana Wata Ma'aikaciya Sanya Hijab A Faransa
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Malta
      • Photos: An Kaddamar Da Sarkin Kano Mastayi Sabon C...
      • Photos: Gwamna Jihar Nasarawa Ya Kwanta Akan Katif...
      • Nafisah Abdullahi Tayi Allah Wadai Da Matan Da Ke ...
      • Photos: Happy Birthday Haleema Atete, Ga Sabin Hot...
      • New Film : Zurfin Ciki 2015 Part 1 Starring Ali Nu...
      • An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambia
      • Magajin Garin Kano Ya Rasu
      • Photos:Buhari,Osinbajo, Saraki, Tinubu Da Amaechi ...
      • Video: Manchester United 0 PSV 0
      • Video: Shakhtar Donesk 3 Real Madrid 4
      • Yanda Ake farfesun kifi
      • Yanda Ake Karya Sihiri Da Lalata Sharrin Aljanu
      • Photos: Buhari Ya Halarci Wajen Binne Matan Awolowo
      • Za A Fara Kama Masu Boye Fetur A Najeriya
      • Abu Ashirin Da Mata Ke So
      • Macen da Aljanna ta fi Karfin ta
      • New Music: Nayi Kira By Hussaini Danko
      • New Music : Kira Nake by Hussaini Danko
      • Yanda Ake Hada Kunu Aya
      • Al'ajabi Part 11
      • Paparoma zai je Kenya
      • An gano wata jigidar bama-bamai a Paris
      • Bangladesh ta haramta amfani da Facebook saboda Tsaro
      • Graphic Photos: Abunda Kishiyarta Ta Mata Ranar Am...
      • Hanyoyin 15 Da Zaka Bi Domin Gujewa Aikata Zinna
      • Al'ajabi Part 13
      • Al'ajabi Part 12
      • Video: Barcelona 6 Roma 1
      • Video: Arsenal 3 Dinamo Zagreb 0
      • Video: Maccabi Tel-Aviv 0-4 Chelsea
      • Photos: An Ba wa 2face Sarauta A Kaduna
      • Buhari Ya Bada Sakon Ta’aziyya Ga Iyalan Audu
      • APC Za Ta Tsayar Da Sabon Dan takara
      • New Music: Mafita By Hussaini Danko
      • New Music: Rabin Mutum By Hussaini Danko
      • Al'ajabi Part 14
      • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
      • Graphic Photos: Wata Yarinya Tana Bukatar Taimako ...
      • Hakurin Zama Da Mace Mara Biyayya
      • Photos: Aisha Buhari A Offishin FIRST LADY
      • Photos: Major AL Ayangbesan, Soja Najeriya Wanda B...
      • Boko Haram, ISIS, Al-Qaeda Na Shirin Kai Hari — Am...
      • Photos: Sabin Hotuna Iyalan Marigayi Sani Abacha
      • New Music: Shakuwa By Hussaini Danko
      • Photos: Buhari Ya Halarci Taron Kasashen Masu Arzi...
      • An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh
      • Darussa Bakwai Game Da Rasuwar Dan Takarar Gwamna...
      • Photos: Isar Buhari Iran
      • Abunda Dokar Zabe Tace Akan Mutuwar Audu
      • An yi jana'izar Abubakar Audu
      • Mutane 8 sun mutu a harin Maiduguri
      • Film: Download Hausa Shargalle Part 2 Starring Sul...
      • Photos: Adama Indimi A Sabon Hotuna
      • New Music: Sirrina By Hussaini Danko
      • Photos: Ali Artwork Ya Ziyarci Rahma Sadau
      • Prince Abubakar Audu Dan Takara Gwamna Jihar kogi ...
      • An Kai Hari A Garin Kauye Mafe Dake Borno
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Iran
      • Photo; Aisha Buhari, Ambode Da Bola Tinubu Wajen W...
      • Film: Download Hausa Film Shargalle Part 1
      • Al'ajabi Part 10
      • List: Makarantu Sakandare Da Suka Fi Kowani Makara...
      • Photo: Buhari Tare Da Tsohon Direban Sa Da Yar sa
      • Music: SO by Hussaini Danko
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • The Missing seven-year-old boy found dead in Kano
    Seven-year-old Khalifa Saminu Saleh was tragically found deceased six days after he was reported missing in the Kuruma community...
  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Rikicin Tsakanin Hadiza Gabon Da Zaharadeen Sani ( Bayanai Da Rahoto) S...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger