1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Arewa » Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida gidansa fadar Shekau – Balaraba Abacha

Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida gidansa fadar Shekau – Balaraba Abacha

By Abdul Mk
Add Comment
Sunday, 28 June 2015

A ranar 5 ga Agustan bara ne mayakan Boko Haram suka suka kwace garin Gwoza da ke Jihar Borno tare da ayyana garin a matsayin hedkwatar Daular Musulunci a Afirka ta Yamma a karkashin jagorancin Abubakar Shekau. A lokacin da mayakan Boko Haram din suka kwace garin sun kone wani bangare na fadar Sarkin Gwoza lamarin da ya sanya suka nemi wani gida na daban don kasancewa gidan da Shekau zai zauna. Gidan Alhaji Aliyu Abacha da ke garin Gwoza ne mayakan suka zaba a karshe, kuma matarsa Malama Balaraba Aliyu Abacha ta shaida wa wakilinmu faru yadda lamarin ya faru kamar haka: Ranar Talata da 5 ga Agustan bara da yamma muna zaune lafiya, kwatsam, sai ’yan Boko Haram a karkashin jagorancin shugabansu Abubakar Shekau da ayarin motocinsa kimanin hamsin da wasu a kan babura suka farmaki garin Gwoza, inda jama’a suka watse suna gudun tsera da rai maza da mata. Mai gidana ya ruga da gudu ya hau katanga domin ya tsera da ransa, amma sai kaddara ta riga fata ya fadi ya karye a kafa. Wannan ya sa aka tallafa masa inda surukarsa wato mahaifiyata ta kai shi gidan surukinsa wato gidan mahaifinmu.”
Malam Balaraba ta ci gaba da cewa: “Sai ’yan sharar fage na ’yan Boko Haram din suka shigo gidanmu suka ce matan da ke gidan wato gidan Aliyu Abacha su fice domin Amir wato Shekau zai shigo gidan kuma dakin Balaraba ne aka zaba masa don ya zauna a ciki wato gidan mijina ya zamo sabon fadarsa saboda sun kone wani bangare na fadar Sarkin Gwoza a lokacin.”
Ta ce gidansu babba ne da ke dauke da kayan alatu. Kuma mayakan Boko Haram din sun ce duk wanda ya yi musu da su, za su aika da shi Lahira, ko kuma su kai shi dajin Sambisa wanda suke kira da rizab.
Balaraba ta ci gaba da cewa ba ta taba ganin Amir din ba, domin yana zaune ne a cikin mota. Kuma jeren motocin da suka yi masa rakiya sun kai motoci hamsin. Sai suka tambayi makullan motcoinsa. Ta gaya musu cewa daya na wurinsa, daya na wurin direba.
Ba su nemi kudi don fansar rai ba:
Balaraba ta ce mayakan Boko Haram ba su nemi a ba su kudi domin fansar rai ba, dalili kuwa shi ne su ran kawai suke nema su dauka, ta ce duk wanda yake namiji dan shekara 10 zuwa 13 zuwa sama, to matacce ne idan suka hadu da shi.
Ta ce bayan ta bar gidan mijin nata: “Ina isa gidan iyayena sai na sume, sai bayan kwana hudu na farfado, sai maigidana ya zo ya same ni a ranar Asabar.”
Balaraba ta ce bayan da mijinta ya karye a korar ta ’yan Boko Haram, sai ta yi niyyar fitar da shi daga garin da misalin da karfe 1:00 na dare a kurar sayar da ruwa. Amma sai maigidanta ya ce ta fitar da yara ta kai wa abokinsa, sai dai ta ce da ta fita kafin ta dawo ’yan Boko Haram sun shiga gidan iyayenta inda mutum biyu daga cikinsu suka ce a bar shi tunda ya karye, amma mutum daya ya ce a kashe shi. Ta ce har sun fita waje sai daya ya dawo ya harbe shi da bindiga a ranar 9 ga Agustan 2014 da La’asar.
“Sai mahaifiyata ta yi kuru ta nufi gidan da Amir yake wato gidan mijina da Abubakar Shekau ya mallake domin ta dauko fararen kaya don a sa masa a matsayin likkafani, amma sai ta ga abin mamaki domin sun dauke kayayyakinsa suna amfani da su. Sai suka ce me ya kawo ta, sai ta ce tana so ta shiga ta dauki fararen tufafinsa ne domin a sa masa don a yi masa jana’iza, sai suka ce in ta kara dawowa gidan za su kashe ta domin “Amir na Gwoza” ba ya son a dame shi. Wannan bayani ya sa mahaifiyata ta tara mata aka binne shi domin babu sauran maza a garin sai tsofaffi marasa gata wadanda babu wanda zai dauke su ko ya ce su taho inda yake. Mu mata kimanin ashirin muka yi masa jana’iza ba wankar gawa a gurguje ba shiri, muka yi addu’a muka yayyafa masa ruwa,” inji Balaraba.
Ta kara da cewa, saboda watsewa da garin ya yi sai suka yi amfani da wuka da ludayin karfe da fartanya suka haka kabari suka binne shi a bayan dakin mahaifiyar matarsa.
Ta ce da ta ga an kashe mijinta sai ta yi tunanin kada su tafi da ’yarsa wacce ita ce ’yar fari mai kimanin shekara 14 wato kada su yi musu abin da suka yi wa ’yan matan Chibok.
Don haka suka yi hijira suka bar garin inda suka yi tafiya a kasa tunda Asuba har sai da dare ya yi sannan suka isa garin Madagali a tsorace ba maganar neman ruwa duk da suna jin kishi da yunwa, ta ce ga gawarwaki ba iyaka a yashe a kasa. Ta ce sun yi kusa da Madagali ne sai ’yan sandan kwantar da tarzoma suka debe su a garin Dumun-Kara aka shigar da su Madagali suka yi kwana hudu.
Balaraba ta ce tana jiran ta ga mahaifiyar marigayi mijinta Aliyu Abacha da aka kashe don ta gaya mata abin da ya faru domin ba ta da labarin ta’addancin da aka yi wa danta.
Ta ce ana nan sai mahaifiyarta ta ce ’yan Boko Haram sun kore s u daga Gwoza, sun je Madagali ba su tsira ba, bayan Balaraba ta yi kwanaki uku da fita takaba sai ta je garin Geidam inda ’yan Boko Haram suka farmaki garin suka watsa su, daga nan ta nufi garin Damaturu a Unguwan Kataro inda bayan makonni uku sai ’yan Boko Haram suka kara tarwatsa su, sannan suka bi mata da ’yan mata da masu ciki suka tafi da su. Ta ce sai ta ce abin da ya fi shi ne tunda ta dan samu lafiya sai ta nufi Kaduna don can tana da ’yar uwa da za ta taimaka mata kafin su koma garinsu.
Ta ce ta nufi Maiduguri daga Kaduna saboda zaman lafiyar da ta yi da kishiyarta domin ta yi mata barkar haihuwar da ta yi a watan Disamba. Ta kuma samu damar rubuta sunanta a cikin ’yan gudun hijira.
Ta ce Haka bayan da Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ci zabe, ta koma Maiduguri domin ta kara rubuta sunanta don an ce gwamnatin Muhammadu Buhari da na Kashim Shettima za su taimaka musu idan an kwato garin Gwoza don su koma nan gaba.
Ta ce abin bakin ciki shi ne da ta hadu da wata makwabciyarsu a Maiduguri ta shaida mata cewa a lokacin da ’yan Boko Haram suka ji sojoji sun nufi garin na Gwoza sai suka banka wa garin wuta gaba daya, inda gidansu ya kone kurmus.
Balaraba ta ce wani karin abin bakin ciki shi ne an aiko mata cewa kishiyarta ta rasu a ranar 9 ga Mayun da ya wuce inda ta bar ’ya’ya biyar. “Yaran a yanzu suna wurin kanen mijinmu wanda matashi ne mai ’ya’ya biyu da ke zaune a garin Damboa, ga shi kuma an kara masa nauyi,” inji ta.
Balaraba ta ce ta yi wata shida ba ta da lafiya sakamakon tashin hankalin da ya so sanya ta zautuwa, sakamakon kashe mata miji wanda ta gan shi ba rai a cikin jini, kuma mata ne suka binne shi a cikin tsoro, sannan an kore su daga garinsu. “Haka ya sa ba na iya yin barci, ga hawan jini sai na sha magani nake iya runtsawa,” inji ta.
Balaraba Abacha ta ce mutuwar abokiyar zamanta a baya-bayan nan ta dame ta matuka. Domin tana tunanin yadda yaran za su kasance ganin marigayi mijinta maraya ne kuma ya mutu ya bar marayu.
A yanzu ta ce ta zuba ido ne dmion ganin yadda gwamnati za ta gyara musu garinsu da gidajensu don su koma Gwoza su ci gaba da rainon marayun da Allah Ya bar musu.

Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 11:15
In Arewa
Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida gidansa fadar Shekau – Balaraba Abacha Title : Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida gidansa fadar Shekau – Balaraba Abacha
Description : A ranar 5 ga Agustan bara ne mayakan Boko Haram suka suka kwace garin Gwoza da ke Jihar Borno tare da ayyana garin a matsayin hedkwatar Daul...
Rating : 5
Related Posts: Arewa

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida gidansa fadar Shekau – Balaraba Abacha"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ►  November (308)
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ▼  June (216)
      • CBN extends deadline for BVN registration
      • Facebook ya bude ofishin farko a Africa
      • Sojoji sun yi wa mata fyade a Sudan
      • Zurfin Ciki 1----1
      • HUKUNCIN AZUMIN WANDA YAYI MAFARKIN SADUWA
      • I don't have a house outside Nigeria - Aliko Dangote
      • Chadi ta yi wa Boko Haram luguden wuta
      • HUKUNCIN JININ HAILA MAI RIKICI
      • Carlos Tevez ya koma Boca Juniors
      • Wikki Tourists ta doke IfeanyiUbah da ci 1-0
      • Hisba ta kama mutane ‘aljannu’
      • Yadda ’yan Boko Haram suka kashe mijina suka maida...
      • Yadda muka yi azumi a kasar Switzerland
      • Tsohon shugaban Nigeria Gowon ya goyi bayan an cir...
      • An kai harin bam a Maiduguri
      • Harin kunar bakin wake ya hallaka mutane 5 a Maidu...
      • RAHOTO Kan Sabuwar Kungiya Mai Kama Da Boko Haram ...
      • HUKUNCIN SAYAR DA KAYAN ADO
      • RASHIN GAMSAR DA MATARSA
      • LABARIN WANI BARAWO
      • TANA AZUMI AMMA BATTA SALLAH
      • SALATUT–TASBEEHI DAGA ZAUREN FIQHU
      • BAI HALATTA KA RIKE KUDIN WANI
      • Buhari ya rushe hukumar zartarwar NNPC
      • MATSALAR CHANZAWAR HALITTA
      • Obama ya gayyaci Buhari zuwa Amurka
      • An yanke wa mutane 9 hukuncin kisa a Kano
      • Musulman China da aka hana azumi sun fafata da 'ya...
      • YADDA ZAKA FITA DAGA DUK WANI TSARI DA MTN SUKE CI...
      • Budurwar da ta yi Tayin Mota da Gida Na Asibiti a ...
      • Yan Boko Haram sun Halaka Mutane 42 A Biu
      • Yadda ake goge account ɗin mutumin da ya mutu a Fa...
      • Liverpool ta saya Roberto Firmino
      • Cutar Kwalara ta barke a Sudan ta Kudu
      • Buhari ya gargadi gwamnoni Akan Cuwa-Cuwa
      • What should the fasting person do and what is obli...
      • Leaving Off Fasting During Ramadhaan Due To Exams ...
      • He had Sexual Relations With his Wife During the D...
      • If a Fasting Person Masturbates, Does This Break H...
      • Using an Inhaler During for the Fasting Person
      • Bleeding from the Mouth/Nose Whilst Fasting
      • She Fasted During Her Days of Menstration
      • Fast what is upon you from missed fasts first
      • Can I kiss my wife while fasting
      • [Music] Download Autar Mata by Nura M Inuwa ft Uma...
      • CIKIN DARE Part 1
      • DUK ABINDA KAKEYI DAKATA KA KARANTA TAMBAYOYIN NAN...
      • YA KAMATA KUJI LABARIN WANNAN MATAR
      • Mata 10 Wadanda Allah Ya Tsine Musu
      • Sabuwar Gwamnatin Najeriya Zata Inganta Rayuwar Na...
      • Arsenal na daf da daukar Petr Cech
      • An umurci soji su cire shingaye a Nigeria
      • Du'a Gamai Azumi Idan Zaiyi Buda Baki.
      • Yadda Zaka Sami Kyautar 1GB A Layinka Na Glo
      • Does Masturbation Break the Fast?
      • Birnin Tsafi [Part 1]
      • President Buhari to remove oil subsidy?
      • HUKUNCIN ORAL SEX
      • TSOKACI AKAN WA'AZI DA MASU YINSA
      • United na zawarcin Ramos da Schweinsteiger
      • Juventus ta dauki Mario Mandzukic
      • Zan yi wa Buhari biyayya — Atiku
      • Bam ya hallaka mutane 20 a Maiduguri
      • Mayakan IS Sun Yi Awan Gaba Da Wasu Limaman Massal...
      • [Pictures ] President Muhammadu Buhari In His Farm
      • President Buhari Moves Into Presidential Villa
      • CIN NAMAN MUTANE DA AZUMI
      • Messi ya jajantawa Neymar bisa jan kati
      • Limamai sun soki daina ciyarwa da azumi
      • Rahmatullah Part 7
      • MAGANIN CIWON MARA
      • Dan-Maraya Jos ya rasu
      • [Tafsir] DR SANI UMAR RIJIYALLEMU
      • [Tafsir]Download Ramadan Day 1 Tafsir By Sheikh Am...
      • [Mp3 Tafsir] Download Ramadan Day 1 Tafsir By Shei...
      • [Mp3 Tafsir] Download Ramadan Day 1 BySheik Kabir ...
      • Dan Marayan Jos Is Dead
      • Kakuta ya koma Sevilla
      • Gwamnatin Bauchi ta kwato motoci 28
      • FIQHUN AZUMI DAGA ZAUREN FIQHU
      • Rahmatullah Part 6
      • SHIN AURENSU ZAI GYARU?
      • Bauchi Govt Seizes 22 Vehicles From Yuguda’s Wives
      • Rahmatullah Part 5
      • SIFFOFIN ALJANNAH
      • SHIN KOYA HALATTA MUSULMI YAYI AIKI A CHOCHI, DON ...
      • ADDU'A GAMAI AZUMI IDAN ZAIYI BUDA BAKI.
      • Sani Musa DanjaYayi Rabon Shinkafa A Kano
      • Kano Pillars ta doke Giwa FC da ci 4-1
      • [MUSIC] Download Kololuwar Fahimta By Naziru M Adam
      • A Touching Hadith About Dua During Iftar
      • Summary Of Things That Nullify A Person's Fast (sawm)
      • FIQHUN AZUMI DAGA ZAUREN FIQHU
      • NAIMAKA RANA PART 10
      • HUKUNCIN CIN NAMAN SADAKAR ALJANU
      • IYAYENTA SUN HANA TA KOMAWA WAJEN MIJINTA
      • Wani dan bindiga ya kai hari a South Carolina
      • Dangote ya dade yana sha’awar Arsenal
      • Bam ya hallaka mutane 23 a Monguno
      • Ni ma ina kaunar Nafisa — Adam Zango
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Suspect - Episode 1 ( Dj Giggs ft J Prince ft Nabs Kid) Hausa HipHop Ser...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • (New Music) Reason By Peevibes
      PeeVibes - Reason Williams Akinsola Precious Popularly known as peevibes has returned again with this mind blowing song tagged “Reason”. T...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...
  • Yadda Kotu Ta Daure Bobrisky Watanni Shida Ba Tare Da Zabin Biyan Tara Ba
    Kotu ta daure Bobrisky watanni 6 ba tare da zabin biyan tara ba Babbar kotu a jihar Lagos ta yanke hukunci ga Idris Okuneye da a...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger