1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Kazamar Gida Part 4

Kazamar Gida Part 4

By Abdul Mk
Add Comment
Thursday, 5 November 2015
Ta zuba masa ido tana hankalta da tarin damuwar dake kwance a saman fuskarsa. Adaidai lokacin yake amsa gaisuwar kannensa,sannanya k'arasa har inda mahaifiyarsa ke zaune,cikin ladabi irinta Jafar ya russuna a gabanta ya gaisheta. Hajja ta amsa har lokacin idanuwanta basu kaura daga kan fuskarsa ba. Gefenta ya zauna yana mai yamutsa fuska alamar gajiya.
Hajja ta umarci d'aya cikin kannensa data kawo mishi ruwa.
Saida Jafar yasha ruwan nan mai sanyi sannan ya iya sauke numfashi.
Hajja ta jefo masa tambaya
"Babana menene ya faru na ganka cikin damuwa?"
Jafar ya shafi sumar kansa yana murmushi a wahale
"Babu komai Hajja,Siyama ce bataji dad'i ba. Ina kasuwa anti rumaisa ke sanarmin,a asibiti ma na iskesu har Hajiya. Amma jikin yayi sauki sun maidata gida."
Hajja cikin nuna jimami tace
"Assha, ai fa naji yarannan sunce Rumaisa tazo sun fita da Hajiyar(dayake gidansu Jafar da nasu Siyama suna facing juna) ashe wajenta suka nufa,meya samu ita Siyamar?"
Jafar ya d'an tab'e baki
"Wai juna biyu take dauke dashi."
Cike da mamaki hajja take dubansa
"Wai fa kace?"
Yayi saurin gyara zancen
"A'a,juna biyun ne Hajja."
Ta saki fuska "Alhamdulillah,nayi murna. Allah Ya rabasu lafiya,saika kula da ita sosai don Allah."
Jafar ya gyada kansa,Hajja dai ta lura ba rashin lafiyar Siyama kad'ai bane damuwar Jafar,don haka tace
"Babana akwai abunda ke damunka bayan wannan,ka sanarmin menene ke faruwa? Idan bani da maganin abun sai na bika da addu'a."
Tayi shiru cikin yanayin damuwa,ba yau ne farkon fara ganinshi cikin yanayi haka ba saidai batason sanya ido duk da tana zargin zamantakewarsu da Siyama sanin halin da akayi auren Hajiyarta bataso.
"Hajja bakomai,kaina yake ciwo ne. Ina kasuwa rashin lafiyar Siyama ya taso ni,amma yanzu komai da sauki. Idan da abinci a zubomin."
Ya k'arasa yana kwantar da kansa jikin kujera,idanuwansa a lumshe,bayason ganin hajjarsa cikin damuwa ko yaya ne balle kuma ace sanadinsa ne ta shigeshi. Yana ji sadda tace"Allah Ya yaye maka." A zuciyarsa ya amsa,ta kwalawa kanwarsa kira sannan ta bata umarnin kawo mishi abinci. Jafar kuwa ya rasa takaiman abunda zai kokawa, bakaken maganganun da Hajiya ta gasa mishi ko kuwa da KAZAMAR GIDAnsa? Dakyar ya iya k'ok'arin had'iye damuwarsa saboda ganin Hajja tana neman sanyawa kanta tunani duk a dominsa.
Bai bar gidan ba sai bayan isha'i bayan ya shiga sun gaisa da Alhajinsa yake sanar dashi dalilin barinsa shago da wuri. Alhaji yace sam,basuyi waya da ibrahim ba ballantana ya sanar mishi. Shima yayi farin ciki da cikin Siyama a karshe sukayi sallama ya tafi ko kallon gidansu Siyama baiyi ba tunda yasan Abbanta baya garin don haka babu sauran wanda zai shiga dominsa.
**************
Koda ya dawo ya sameta tana baccin a d'akinta. Ya rufeta saboda sanyi sannan ya wuce d'akinsa. A daren bacci b'arawo ne kawai ya saceshi.
******
Tun Jafar yana daurewa Siyama har yazo ya share zancen suka d'inke kamar basu ba.
Matsala ta farko daya soma cin karo da ita tun samun cikin Siyama,bai wuce k'azantar jikinta daya k'aru ba. Dole ya kauracewa hada shimfid'a da ita,idan kuma yaga cutar zatayi mishi yawa yakan rok'eta akan ta taimaka tayi wanka,harma da kanshi ya d'ora mata ruwa,sai ta gama kumbure kumburenta zatayi,kamar da gaske za'a d'ore a hakan sai kuma ta bar yi. Koda ya dora ruwan hakanan saidai ya hakura. Akan dole ya sabarwa kansa da azumin litinin da alhamis. Sunfi sati uku rabon da wata mu'amalar kwanciya ta shiga tsakaninsu,hakanan kowannensu yana nasa d'akin.
Siyama ta bar yin kowane gyara ga jikinta,idan kuwa unguwa ta kamata saidai ta goge hammatarta da ruwan alimun da lemun tsami,alokacin ne zata kokarta ta sharce gashinta wanda Jafar bai tab'a ganinsa a kitse ba. Duk wani kwaskwarima Siyama tasan yanda zata yishi muddin ta tashi fita unguwa.
Yanzun ma fitar ce ta taso mata,wai zataje gidansu daganan su wuce biki can a dangin hajiyar tasu. Yana tsaye gaban madubin d'akinsa yana aikin gyara sumarsa,ta shigo d'akin. K'amshin da yaji ya bugi hancinsa ne ya sanyashi waigowa. Murmushin takaici yayi ya k'are mata kallo tun daga k'asa har sama. Anci riga da siket,fuskar nan an wanketa da kwalliya daidai da zamani. Bai tab'a sanin ta mallaki kyakkyawan leshin nan ba sai a yau. Ya ganta tamkar Siyamarsa sak ta baya, abun bakin ciki harda wadannan kwalliye kwalliyan aka yaudareshi baisan kyallin banza bane.
Murmushi ta jefeshi dashi,ya girgiza kansa yana tab'e baki kafin ya juya ya cigaba da shirinsa. Hannuwanta yaji ta bayanshi
"Jafar banji kace nayi kyau ba?"
Ya lumshe ido ya bude,ta madubi suka kalli juna. Murmushi ya k'ara yi a karo na biyu
"Kinyi kyau,da ace haka kike zama a gidanki da ba haka ba. Kwalliyarki ai ta fita unguwa ce."
Ta sakeshi ta jingina da bango yayinda take dubanshi yana zura riga
"Jafar kenan,nikam kana bani mamaki yanda bakason yimin uzuri. Baka ganin yanda nake fama da kaina? Kwalliyar ma dole ce ta sanyani yinta a yanzun,kowane sutura zan saka inajin kaina a takure wallahi."
"Siyama kenan,kafin ki samu cikin kuma menene yake hanani yimin? Ko an fadamaki mazan waje sun fini bukatar kwalliyarki? Burinki ki k'ure adaka ki fita amma bakisan kiyimin a gida ba ko?"
Ya tabe baki yana daga kafada
"Ai shikenan,zan auro wacce zata dunga bani kulawa."
Ai saita daure fuska
"Zaka fara ko? Daman ku maza duk abunda matanku zasuyi maku bakwa tab'a gani. Duk kokarin da nakeyi baka gani Jafar. Ni banyi korafin yanda bakason cin abincina ba matukar ba shinkafa da wake nayi ba,sai kai keda bakin cewa banason yi maka kwalliya? Sau nawa ka bani kud'in kayan kwalliyar?"
Jafar dake shirin sanya hula ya tsaya cak yana kallonta,mamakima ta bashi. Ta dauke idonta daga gareshi fuskarta a kumbure
"Siyama har kina da bakin gayamin haka? Ai kuwa idan har kika shaideni akan bana siya maki kayan kwalliya duk da har yanzu akwai sauran na lefenki bakiyi adalci gareni ba. Hakanan sau nawa na baki kud'in wanke gashi kike biyan bashi dasu? Sau nawa kikayimin karyar zakiyi kunshi na ciro kud'i na baki,kin tab'a yi? Bani mantawa bikin Kawarki daya tashi kad'ai ne sadda na soma ganinki da kunshi a kafarki tun bayan na bikinki daya goge. Siyama ke ta dabance ma acikin kazaman matan,bansan irinki ba! Girkin da kike magana a zatonki zan iya cin cima marar dad'in d'and'ano ne? Ke komai da mata sukeyi ke bakiyinsa,baki iya ba sai afkin karance karance da kallace kallace. Duk a banza Siyama,banga amfanin ilimin boko dana arabin da kikayi ba. Bazan iya cigaba da zama kodayaushe ina yawon zuwa gidan abinci ba,ya rage naki ki gyara kanki ko kuma abunda kike gudu ya faru."
Har ya kai k'arshe bata da niyyar cewa komai. Binsa kawai takeyi da kallo,fargabanta ya k'aru. Kada dai ace dagaske Jafar auren zaiyi? Tana ganin ya fita waje, tayi saurin daukar wayarsa. Duk iya lalubenta bata ci karo da lambar wata budurwa ba 'bare' wacce bata sani ba yan uwansu ne zallah wadanda itama ta sansu. Tana shirin duba b'angaren sak'onni ya shigo. Yana kallonta saima ta bashi dariya yayi murmushi
"Fito muje,ba saikin wahalar da kanki ba Siyama. Bani da budurwa bana sha'awar yin wani auren amma ina sha'awar mace mai tsafta wacce ta iya girki da kwalliya. Wacce zata bani kulawa da girmana a matsayin mijin aurenta. Matukar zaki zama irin haka toh wallahi fargaba ba naki bane,domin babu macen da zata burgeni. Ke kanki kinsan bana ra ayin mata biyu. Amma kuma a yanzu na soma chanja ra ayi matukar bazaki gyara ba."
Ya d'auki wayarsa data ajiye,ko kallonta baiyi ba ya fito.
"Kin tsaya,nace ki fito zan rufe d'akin ko?"
Ta fito a sanyaye tana duban fuskarsa dake a had'e,ya rufe d'akin gam da mukulli tayi azamar riko hannuwansa. Bayason duban kwayar idanunta yanzun nan sai fushinsa ya sauka. Ta narkar da murya
"Jafar nasan bana kyautata maka,kayi hakuri don Allah. Ni yanzu ya kakeso nayi? Duk ka sanyayamin jikina Jafar,kaima kasan ban taba son wani mahaluki ba saikai,irin son da ko kusa bana marmarin wata ta kusanci inda..."
Ya katseta yana dariya,wallahi Siyama fa ta rainashi. Yo banda raini har ma ta tsaya tana tsarashi akan abunda yasan ba gaskiya bane. Shi yasan ba kud'i ne dashi ba sai rufin asirin Allah,ba wani kyau ne dashi ba na azo a gani domin a kyawun ma Siyama ta tsereshi ba kusa ba. Zai iya yarda tana sonshi saidai bayan aurensu ta rage sonshi tunda har bazata iya faranta mishi ba hakanan sonta ya ragu a zuciyarsa saboda sabbin halayenta da yaci karo dasu bayan auren.
"Kina b'atawa kanki lokaci,kin sameni ina bacci kin matsamin nayi sauri nayi wanka ana jiranki,yanzu kuma zaki tsaidani ina fa da wurin zuwa Siyama. Taho mu wuce,idan muka dawo sai ayi maimaicin karatun ko Allah zai sa yau nayi dace."
Ya janye hannuwansa yayi gaba,ta bishi a baya gwuiwa sake.... !
Zaune suke akan benci gaban gidan amininsa,Haris.Kwanansa d'aya da dawowa daga Gusau garin iyayensa. Hira sukeyi na bayan rabuwa,Haris yace
"Ina amarya Siyama? Ka k'i kawota su gaisa da Ummina ko?"
Ya harareshi
"Ita Ummin meya hanata kawo mana ziyara?"
Haris yayi dariya
"Zaka take gaskiya kenan? Ummina fa zuwanta biyu gidan a rufe ba kowa kodai ka manta ne? Idan zumuncin na gaske ne kaine yafi dacewa ka dauko Siyama itama tasan hanyar gidana."
Jafar ya mutsistsika hancinsa
"Wannan kuma sai damar hakan ta samu. Ni yanzu ka saurareni inada muhimmin batun da nake neman shawararka akai."
Haris ya nutsu yana gyara zaman 'medical glass' d'insa
"Ina sauraronka."
Jafar ya numfasa ya labarto mishi kad'an daga cikin matsalar da yake fuskanta a wajen Siyama. Ya k'ara da cewa
"Nifa na soma gajiya Haris,a ganina lokaci yayi da zan sanarwa iyayenmu. Watakila idan anci sa'a ta ji maganarsu."
Haris kallonsa kawai yakeyi,tun soma jin irin matsalolin da amininsa ke fuskanta, ya gyara zaman gilashinsa yafi sau biyar. Ba don shi da kansa ke sanar mishi ba babu abunda zai hanashi k'aryatawa. Bayan kammala sauraron Jafar yafi mintuna biyu kafin ya motsa bakinsa.
"Jafar kana nufin dukkan abubuwan daka lissafo halayan Siyama ne babu abunda ka k'ara akai?"
Jafar yayi murmushi
"Da ace kasan Jafar a makaryaci Haris,shine zakayi wannan tunanin. Kai shaida ne akan son da nake yiwa Siyama,ta yaya zanyi mata k'age? Haris shawara zaka bani,menene ya kamata nayi na kawo k'arshen matsalar nan?"
Haris ya numfasa
"Kaicon Siyama,na tausayawa rayuwarka Jafar. Babbar matsala ce wannan wanda ba kowane namiji ne zai iya juriyarsa ba. Hakika cigaba da rayuwa a haka ba shine mafita ba,baka da laifi ko a wurin Allah tunda har kayi mata nasiha ka kuma bita da fad'a amma duk da hakan tak'i chanjawa. Shawarar da zan baka itace,ka kai maganar zuwa ga yayarmu anti Habiba(firstborn a d'akinsu Jafar). Ka fayyace mata komai na tabbata bazata rasa taimakon da zatayi gareka ba amma kada kace zaka sanarwa iyayenku,ka manta da yanda akayi auren ne ba'a son ran Hajiya da wasu ba? Ko kuwa so kake ayi maku dariya?"
Jafar ya jinjina kai,hakika shawara ma tana da dad'i. Ba da ban Haris ba,da tuni ya aikata ba daidai ba.
"Hum,damuwa ta sanyani gaza yin tunani mai kyau. Inda ace baka tunasar dani ba,nasan bazan bi takan anti habiba ba. Nagode da wannan shawarar,in sha Allah gobe zanje har gida na sameta."
Haris ya amsa
"Yauwa kokaifa,kasan fa halin wasu matan,yanzu kana kai k'ararsu maimakon su shiga taitayinsu sai wani sabon salon ya b'ullo. Gwara abi abun sannu sannu ko Allah zaisa a dace. Wallahi abun bai bar bani mamaki ba."
Jafar ya girgiza kansa
"Don baka gani bane,ni nasan yanda nake fama. Wai kuma a hakan ne ake cewa ana kishina."
Haris yayi dariya
"Kaicon Siyama,Allah Ya gyara."
"Ameen.
Please like Us On   Facebook
Follow us on   Twitter


Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 14:40
In Hausa Novels
Kazamar Gida Part 4 Title : Kazamar Gida Part 4
Description : Ta zuba masa ido tana hankalta da tarin damuwar dake kwance a saman fuskarsa. Adaidai lokacin yake amsa gaisuwar kannensa,sannanya k'a...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Kazamar Gida Part 4"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ►  December (182)
    • ▼  November (308)
      • Kafin Kayi Barci
      • Yanda Ake Hada Lemon Juice
      • Yan Boko Haram Sun Sace Wasu Mata A Banburaitai
      • Photos: Buhari Ya Isaa Paris Dan Halartar Taron Sa...
      • Ana Ta Samun Nasarar Kwato Shanun Sata a Kano
      • Zargin Kinshiyoyin Ta Sun Mata Asiri
      • Al'ajabi Part 16
      • Hisbah Ta Kama Wani Dan Sanda Da Yi Wa Budurwa Ciki
      • An kaiwa 'yan Shi'a hari a Masallaci a Bangaladash
      • Video: Download Highlight Leicester City 1 Manches...
      • Video: Download Highlight Barcelona 4 Real Sociedad 0
      • Yanda Ake Hada Cake
      • Photos: Yusuf da Zahra Buhari Su Halarci Taron Yay...
      • Photos: Sabin Hotuna Shahida Sanusi Lamido Sunusi
      • Buhari Ya Nada Sabun Alkalai
      • Al'ajabi Paart 15
      • Yan Boko Haram Na Shirin Kaima Abuja Hari
      • Mummunar Shiga Mai Bayyana Tsaraici Da Yan Uwa Mat...
      • New Music: Inda Rai Darabo By Hussaini Danko
      • Graphic Photos :Adadin Mutanen Da Su Ka Rasu A Har...
      • Photos: Gwamna Jihar Bauchi Ya Ziyarci Atiku Abubakar
      • Graphic Photos:Yanayi Wanda Ya Kai Hari Yau A Jiha...
      • Tafsir: Rikicin Duniya Da Na Lahira By Sheikh Isa ...
      • Hanyoyin 25 Masu Sauki Domin Samun Lada Mai Yawa
      • New Music: Kana Raina By Hussaini Danko
      • Bom Ya Tashi Dan Yan Shi'a 15 A Kano
      • Photos: Buhari Ya Gana Da Sarauniyar Ingila A Malta
      • Tafsir: Tambayoyi Tara Bayan Mutuwa By Sheikh Isa ...
      • Graphic Photos: Wani Dalibi Poly Ya Kashe Kansa
      • Buhari Na Neman Jefa Kasar Nan Cikin Mummunan Hali...
      • Yadda Wani Attajiri Ya Yi Wa Kansa Yankan Rago A J...
      • New Film: Zurfin Ciki 2015 Part 2 Starring Ali Nuhu
      • Yan Najeriya Sun Nuna Bacin Ransu Da Buhari
      • Dan Marigayi Audu Abubakar Ne Zai Maye Gurbin Sa A...
      • Kotu Ta Hana Wata Ma'aikaciya Sanya Hijab A Faransa
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Malta
      • Photos: An Kaddamar Da Sarkin Kano Mastayi Sabon C...
      • Photos: Gwamna Jihar Nasarawa Ya Kwanta Akan Katif...
      • Nafisah Abdullahi Tayi Allah Wadai Da Matan Da Ke ...
      • Photos: Happy Birthday Haleema Atete, Ga Sabin Hot...
      • New Film : Zurfin Ciki 2015 Part 1 Starring Ali Nu...
      • An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambia
      • Magajin Garin Kano Ya Rasu
      • Photos:Buhari,Osinbajo, Saraki, Tinubu Da Amaechi ...
      • Video: Manchester United 0 PSV 0
      • Video: Shakhtar Donesk 3 Real Madrid 4
      • Yanda Ake farfesun kifi
      • Yanda Ake Karya Sihiri Da Lalata Sharrin Aljanu
      • Photos: Buhari Ya Halarci Wajen Binne Matan Awolowo
      • Za A Fara Kama Masu Boye Fetur A Najeriya
      • Abu Ashirin Da Mata Ke So
      • Macen da Aljanna ta fi Karfin ta
      • New Music: Nayi Kira By Hussaini Danko
      • New Music : Kira Nake by Hussaini Danko
      • Yanda Ake Hada Kunu Aya
      • Al'ajabi Part 11
      • Paparoma zai je Kenya
      • An gano wata jigidar bama-bamai a Paris
      • Bangladesh ta haramta amfani da Facebook saboda Tsaro
      • Graphic Photos: Abunda Kishiyarta Ta Mata Ranar Am...
      • Hanyoyin 15 Da Zaka Bi Domin Gujewa Aikata Zinna
      • Al'ajabi Part 13
      • Al'ajabi Part 12
      • Video: Barcelona 6 Roma 1
      • Video: Arsenal 3 Dinamo Zagreb 0
      • Video: Maccabi Tel-Aviv 0-4 Chelsea
      • Photos: An Ba wa 2face Sarauta A Kaduna
      • Buhari Ya Bada Sakon Ta’aziyya Ga Iyalan Audu
      • APC Za Ta Tsayar Da Sabon Dan takara
      • New Music: Mafita By Hussaini Danko
      • New Music: Rabin Mutum By Hussaini Danko
      • Al'ajabi Part 14
      • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
      • Graphic Photos: Wata Yarinya Tana Bukatar Taimako ...
      • Hakurin Zama Da Mace Mara Biyayya
      • Photos: Aisha Buhari A Offishin FIRST LADY
      • Photos: Major AL Ayangbesan, Soja Najeriya Wanda B...
      • Boko Haram, ISIS, Al-Qaeda Na Shirin Kai Hari — Am...
      • Photos: Sabin Hotuna Iyalan Marigayi Sani Abacha
      • New Music: Shakuwa By Hussaini Danko
      • Photos: Buhari Ya Halarci Taron Kasashen Masu Arzi...
      • An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh
      • Darussa Bakwai Game Da Rasuwar Dan Takarar Gwamna...
      • Photos: Isar Buhari Iran
      • Abunda Dokar Zabe Tace Akan Mutuwar Audu
      • An yi jana'izar Abubakar Audu
      • Mutane 8 sun mutu a harin Maiduguri
      • Film: Download Hausa Shargalle Part 2 Starring Sul...
      • Photos: Adama Indimi A Sabon Hotuna
      • New Music: Sirrina By Hussaini Danko
      • Photos: Ali Artwork Ya Ziyarci Rahma Sadau
      • Prince Abubakar Audu Dan Takara Gwamna Jihar kogi ...
      • An Kai Hari A Garin Kauye Mafe Dake Borno
      • Photos: Buhari Yabar Najeriya Zuwa Iran
      • Photo; Aisha Buhari, Ambode Da Bola Tinubu Wajen W...
      • Film: Download Hausa Film Shargalle Part 1
      • Al'ajabi Part 10
      • List: Makarantu Sakandare Da Suka Fi Kowani Makara...
      • Photo: Buhari Tare Da Tsohon Direban Sa Da Yar sa
      • Music: SO by Hussaini Danko
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Zuwa Da Budurwa Yawon Duniya ( Kalli Kaci Dariya)
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Innalillahi wainna illaihin rajiun - Allah Yayi Wa Mawaki Aliyu Sharba R...
  • Sadiya Gombe Ft Al'ameen Bauchi (Ra'ayin Ki Ne Nawa) Sabuwar Waka
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • Bikin Aure Abubakar Bashir Maishadda Da Hassana Mohammad
     Ana Shirin Auren Furodusa Abubakar Bashir Maishadda da jarumar kannywood Hassana Mohammad Ga Zafafafa Hotunan Bikin youtubeem...
  • The Missing seven-year-old boy found dead in Kano
    Seven-year-old Khalifa Saminu Saleh was tragically found deceased six days after he was reported missing in the Kuruma community...
  • Fantyz Guy ft Mr SPYZY - ALKALERI GARINA (Official Hausa HipHop Music Video...
        Bauchi Base Popular HipHop musician FANTYZ GUY release hit track ALKALERI GARIN Featuring Mr SPYZY 

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger