1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog
  • Home
  • Arewa
  • News
  • Kannywood
  • Music
  • Videos
  • Islamic
  • Sport
» Hausa Novels » Al'ajabi Part 17

Al'ajabi Part 17

By Abdul Mk
Add Comment
Tuesday, 1 December 2015
Na karasa kai wayar kunnena yalwataccen murmushi na tashi daga fuskata, sai dai tayi saurin canjawa daga annuri zuwa rashin fahimta sanda naji muryar dana tbbtr ba tashi bace.
Idan har a yadda muka fahimta dai-daine Ga alama kece matar me wayar nan ko??
Ckn y‘an sakannin da yayi na maganar 2n kafin yakai karshe fuskata ta rikide daga yadda take a baya zuwa mummunan yanayin daya wuce misaltawa nayi saurin cewa “Eh...eh nice la..fiya meye ya faru??“
ka2war muryar tamkar ana buga diro dake magana tayi shiru zuwa can tace “To kiyi gaggawar zuwa asibitin SABO TAIWO HOSPITAL mijinki ya samu mummunan accident...“
Iya abnd kunnuwana suka iya jiye min kenan suka dauke dif ma‘ana suka daina jin komai, wani duhu ya ziyarci idanuna na daina ganin inda nake tsaye ma bare nesa. Kaina kuwa wata irin juyawa ya fara yi kwatankwacin yadda belt din inji ke juyawa sanda yake aiki, wani gumi me zafi ya fara ketowa ta ko‘ina daga jikina tamkar an watsa min ruwan zafi.
(wani yasaman yacemin wai ina tsalleke..to ni ban tsallake duk wanda be gani haq qarke to se ya koma ta opera zegani har inda mu ka tsaya..)A tsaye nake na kasa gaba na kasa baya, a takaice dai gaba daya na dauke wuta, ni kaina banyi yunkurin motsawa ba don nasan faduwa ce zata biyo baya saima mika hannuna da nake yi wai ko zanji bango na dafa amma babu. Na shiga yanayi mafi muni 2nda uwata ta haifeni yau sanadin MUMMUNAN ALBISHIR!!
Bansan sanda wayar ma dake hannuna ta subuce zuwa kasa ba, tana dira kuwa ta tarwatse komai nata ya rabu da dan uwansa, na dade a tsaye tamkar gunki dafe da kaina dake juyawa.
Zuwa jimawa kadan dana ji dan dama-dama na yunkura da karfi daga inda nake tsaye wani jiri ya kwasheni ta gefe nayi kasa sai dai bisa sa‘a jina kawai na fado akan kujera, na dunkule kaina na fashe da kuka hawaye na zuba tamkar ruwan sama.
Zaiyi wuya in ban rasa faruk ba. 2nanin da nayi kenan wanda yasa nayi gaggawar mikewa duk da ban gama dawowa dai-dai ba na jawo mayafina, takalmina da mukullin motar faruk duk na rikesu a hannuna nayo waje da gudu.
Banma yi yunkurin tsaida kukan da nakeyi ba don nasan bame yiwuwar tsayawa bane.
ganin a yanayin dana fito yasa salih tasowa tare da tambayar “hajiya lfy??
ya na ganki haka??
me ya faru kike kuka kuma??
Na daga baki dakyar nace “Faruk ne.. sunyi accident yanzu haka suna...asibiti...“
Nakai karshen maganar dakyar.
Subhanallahi!! Accident??
shima ya fada a gigice, hankalinsa ya tashi ma2ka.
Yayi saurin amsar mukullin dake hannuna ya bude min kofar motar, muna shiga ya juyar da ita muka fice.
Duk da gudun da salih keyi iya krfnsa amma na raina gudun ji nake kmr na sauka na ruga da gudu, kuka kawai nake rusawa 2n salih na bani hakuri har ya gaji ya daina.
Muna isowa harabar asibitin kukana ya karu 2n kafin ya gama tsayawa nayi ready na sauka, yana tsayawa nayi yunkurin fita yayi saurin dakatar dani da fadin “hajiya kiyi hakuri ki rage kukan nan don Allah ki samu nutsuwa ko yayane, dubi yadda kike fa!!
Nabi mayafina da takalmina wadanda duk suke rike a hannuna nabi shi da kallo kawai na saki takalmin zuwa kasa na zirashi ckn kafata na yafa mayafin akan kafata kawai nayo waje nayi saurin tsayawa sakamakon motar dana gani a nesa kadan dani na ganeta motar tasin da faruk yahau ce, gaba daya tayi raga-raga lallai ba karamin accident bane.
Nan fa na sake rudewa da firgici me tsananin, ‘IHHH!!!! bakina ya furta dai-dai sanda hakorana suka fara karo na sama na dukan na kasa ji kake KAF! KAF! KAF! jikina yadau tsima.
nasan zaiyi wuya wanda ke ckn motar nan ya fita da rai, na juya da gudu izuwa ckn asibitin bangaren Emergency na nufa don nasan bazai wuce can ba, 2n kafin na karasa naga an fito da wani daga daki bisa irin gadon nan da ake 2rawa an lullube jikinsa alamun ya mu2.
kawai ji nayi kafafuna sun dakata, SHIKENAN!! ya mutu!!
kukana ya canja salo, da sauri na tari gaban wadanda ke 2ra dan siririn gadon na dire a gabansa tare da bude mayafin dake rufe da fuskarsa.
Nadan yi baya a zaune KAI! ba faruk bane!! na ganeshi direban tasin ne.
Nayi wata juyawa a haka na mike tsaye da gudu na doshi dayan dakin dake kusa da wanda naga an fito da wancan.
Kai tsaye na fada da yake dakin nada zurfi zarcewa nayi zuwa tsakiyarsa, tfyt tayi saurin cnjw na koma tfy a hankali sabanin gudun da nake yi a baya.
Har na karaso gbn gadon da yake kwance, kwance yake idonsa a rufe tamkar meyin barci gaba dayan kansa na nade da farin bandeji, hannunsa dama kafarsa.
Numfashinsa na hawa da sauka a hankali, y‘ar farar kyakykyawar fuskarsa na klln sama.
Na tsaya akan gadon nasa na zuba masa ido da yanayin da yake ciki, nabi pipe na ledar karin jinin dake jone a jikinsa da kallo sama inda take rataye.
Wasu hawaye da suka banbanta da nadaa suka zubo min, Bai mutu ba.
Abinda na baiwa kaina tbbs kenan.
Na cake gwiwoyina a kasa na dora kaina bisa gadon gefensa kadan na zarce da kuka me tsanani, wanda duk wanda yaji sai ya tausaya min.
Na jima a haka ko sau daya ban dago kai ba, ji kawai nayi an dafa bayana a hnkl na dago kai muka hada ido da wata siririyar farar nurse dake sanye da fararen kaya, tayi murmushi tace “am sorry dan matsa kadan zan cire masa wannan ledar.
Na bita da kll da jajayen idanuna kawai na mike wani jiri yaja ni zan fadi nurse din ta taro ni da fadin “hankali zaki fadi fa.“
Na lallaba na zauna a kujerar dake gaf da gadonsa na kwantar da kaina a jkn bango hawaye suka cgb da sintiri a kuma2na.
Nurse din ta cire ledar jinin ta jona masa ledar karin ruwa, tadan tako kmr zata wuce sai kuma ta tsaya ta dubeni tace “kiyi hakuri kinji shi ai nashi yazo da sauki ma2ka, karki damu da yawa.“
Takai karshen maganar tare da dafa kafata ta wuce.
hmm... wane kwantar min da hankali ma zata iya yi??
Tayaya hankalina zai kwanta da wannan bala‘in??
Daga wannan sai wannan, murna ta koma ciki kenan takaici yaci uban nadaa.
Wannan wace irin KADDARA ce?? wane irin bala‘i ne??
yaushene zamuyi rayuwa kmr kowa??
ire-iren 2nanin daya mamaye kwakwalwata kenan.
******* ****
Tunane-tunanen nata karo a ckn kwakwalwata, a haka dai naci gaba da zama a kujerar dake gaf da faruk na zuba tagumi tare da kurawa faruk idanu, ba yanayin da yake ciki yanzu nake kll ba amma ainihinsa nake kallo.
kyakykyawar dariyarsa, ingantaccen murmushinsa, da yalwatacciyar fa‘ararsa.
Innalillahi wa inna ilaihir-raji‘un.
Ko a lbr ban taba jin wadanda masifa ta taso su a gaba kmr mu ba, daga wannan sai wannan??
KADDARA!!!
KADDARA!!!
KADDARA!!! itace kawai kalmar dake min yawo a zuciyata.
Domin idan tazo ba yadda aka iya sai dai ayi hakuri a rungumeta, ji nayi kawai dama banma mike nayi tafiya ba faruk ya fita yayi tafiyarsa tuntuni da duk haka bata faru ba. Amma ya muka iya???
Sai da yamma ta farayi sosai sannan ma nayi wani tunanin sanar da wani halin da ake ciki, sai sannan na 2na inda na jefar da wayata can a gida lkcn dana rude sanda lbrn abnd ya faru ga faruk ya isarmin.
Wayar wannan nurse din wadda itace keta zarya akan faruk na ara na kira mufida da nazir bbn abokin faruk da yake umminsa ta tafi umara banyi yunkurin kiranta ba, sai kuma momi dana kira daga karshe.
Momi naji ta rafka salati tare da tambayar “subhanallahi!!
Wane asibitin??“
muna SABO TAIWO HOSPITAL!!
da dan AL‘AJABI ta tambayeni “waye ya daukeki ya kaiki can??“
Bata san halin da ake ciki ba, bata san cewa na dawo dai-dai ba zatonta har yanzu ni gurguwa ce.
Bata samu wata amsa ba saima rushewa dana sake yi da kuka na janye wayar daga kunnena a hnkl, ji nake kmr kaina zai fashe sbd zafi da yayi min.
Mufida ce ta fara zuwa kusan karfe biyar na yammaci lkcn, hankalinta ya tashi ma2ka amma da yake tana da nutsuwa a dan lkc ta fara rarrashina da kalamai masu dadi da saka nutsuwa sai dai ina!!
bata sami kaina ba saima wani kuka daya kara turnuke ni.
Mufida ta rasa yadda zatai dani tadan rike kafaduna tare da cewa “HUMAIRA!! wai me kike so ki zama ne??
Ke ba zaki iya jurar kaddara ba kenan??
Ko kina zaton Haka kawai Allah zai bar bawansa ba jarraba ba.
kuma gsky ta fada fa 2nda faruk dai ba mutuwa yayi ba amma yakamata tasan ba yadda za‘ai koda ciwon kai ya sami faruk hankalina ya kwanta bare hali irin wannan.
daga karshe dai na roketa alfarma da taje gd ta dauko mana wasu abubuwan da zamu bukata, tako mike tare da tambayata ina mukullayen gdn??
Na dan kauda kaina kawai a raina nace gsky wannan ta samu matsala, a ina na sami nutsuwar daukar wani mukulli??
Zuwa jimawa na dubeta da shakakkiyar muryata nace “kije kawai komai a bude yake.“
Ta dan bini da kll kawai tare da girgiza kai cike da tausayawa ta juya ta fice.
Naja kujerata izuwa fuskantar faruk nayi tagumi kawai, ji nake inama nice a kwance bashi ba!!
Ina ma ni masifa ta riska bashi ba!!
ina ma nice hakan ta faru dani bashi ba!!
Sai byn wasu lkt mufida ta dawo, nazir da abkn faruk su uku suka zo, momi ma ba shiri ta bazamo.
Likitan dake kula da faruk ma yayi bayani gamsashshe daya kwantar min da hankali ma2ka, a cewarsa ‘faruk bai sami wata matsala ba saboda kaf ilahirin jikinsa kalau yake iya kansa ne kawai yadan sami buguwa da karfen motar da sukai hatsari akanta shine ma dalilin saka bandejin dake kansa sbd suna tsammanin ko akwai inda ya fashe kuma babu ma hkn yasa bayan wani lokaci suka cire, akwai yiwuwar farfadowarsa nan da wayewar gari.‘
Hakan yasa nadan ji sanyi a raina sosai, tbbs abin yazo da sauki sosai nima na yarda da hakan.
Gefe guda momi dasu nazir AL‘AJABI ya ma2kar turnikesu ganin yadda nake taka kafata tamkar bani ba, na fahimci momi nason tambayata shiru dai kawai tayi.
Sanda dare ya tsala sannan ne duk suka tafi ya rage ni da faruk kawai sai kayayyakinmu daga gefe guda kuma y‘ar hayaniya na tasowa daga waje da yake dakin da muke na musamman ne ba kowa a cknsa sai kuma nurses dake ta kaiwa da komowa don ganin komai ya tafi dai-dai.
Na koma daga can gefen gadonsa na shimfida darduma na fara sallolin nafil-fili da addu‘o‘in samun sauki ga abin alfaharina guda daya tak a duniya, Allah yasa yadda muke tsammani ya zama haka ne.
Addu‘ar dana kwana inayi kenan don ban iya runtsawa ba a daren.
*WASHE GARI*
misalin karfe 10:00 na safiyar ina zaune a kasa bisa shimfidar da nayi nayi tagumi kawai kusan hankalina baya jikina na tafi duniyar 2nani, gwauron numfashin da aka kawo yasa ni dawowa hayyacina na dago kai da sauri na dubi inda sautin ya fito.
FARUK ya farfado!!
abnd na fara fada a zuciyata kenan, nayi zumbur na mike na zauna a gefensa.
fuskata tadan fara saki sanda na tbbtr da abnd nake zato, a hnkl idanunsa suka bude sosai ya yunkura ya mike zaune wani murmushi hade da hawaye suka ziyarceni nadan kawo gwauron numfashi tare da hada hannuna ckn nasa.
Yace “HUMAIRA“ na amsa da “na‘am FARUK!!“
Meya faru dani haka ne??
A ina nake??
kina ina ne ba fitila a inda muke ne?? Nayi saurin sakin hannunsa kirjina ya buga da karfi, kaina ya sara tamkar kwakwalwata zata rushe.
Ba kaganni bane??
Rikici kenan...anya kuwa..
Komeyasameshi..???
Facebook Twitter Google+ Pinterest Linkedin Whatsapp
Posted by Abdul Mk at 12:08
In Hausa Novels
Title : Al'ajabi Part 17
Description : Na karasa kai wayar kunnena yalwataccen murmushi na tashi daga fuskata, sai dai tayi saurin canjawa daga annuri zuwa rashin fahimta sanda ...
Rating : 5
Related Posts: Hausa Novels

LOVED WHAT YOU READ?! THEN DON'T MISS ANY NEW POST! STAY UP TO DATE! SUBSCRIBE NOW!
Join our Subscribers Today and Receive Updates by Mail. We totally hate spam. Your email address will not be sold or shared with anyone else.

Delivered by FeedBurner

0 Response to "Al'ajabi Part 17"

Post a Comment

← Newer Post Older Post ⇒ Home
Subscribe to: Post Comments (Atom)

Video Of Day

Popular Posts

  • Yanda Na Kama Mata Na Aisha Da Nafisa Suna Madigo
    INNALLILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN. A cikin wani hali na takaici da al’ajabi wani magidanci, mai suna Abban Umma ya bayyana yadda ya ...
  • Download Music Komai wuya by Nura M Inuwa
    Click To Download Download
  • Photos: Sabuwar Shigar Aisha Aliyu Tsamiya
       Shahararriyar Jaruma fim din Hausa Aisha Aliyu Tsamiya ta sake sabin hotuna dan sabuwar shigan ta, a shafin ta na Twitter da instagram ...
  • Photos: Sabin Hotuna Nafisa Abdullahi
    shahararriyar Jaruma fim din kannywood Nafisah Abdullahi ta sanya sabin hotuna a shafin ta na Instagram
  • Mijinta Yana Kallon Hotunan Batsa (BLUE FILMS)
    Assalamu alaikum! mallam tambayace daga wata baiwar ALLAH take cewa: mijina ne baida aiki sai kallon hoton mata tsirara. babban abun ...
  • YAYANA MIJINA Part 1
    Sarah ki rike mutincin ki na diya Mace bawai zamu tura ki makaranta dan ki dinga abin da kika ga dama bane, aa kawai dan muna so ki kara kar...
  • ZURFIN CIKI BOOK 4**6
    Ta kyalkyale da dariya, ya Abba yayi santin ruwa, yyi murmushi, naji ne kman kinsa zuma, ya cire takalmashi tre ddora kafafuwanshi akan da...
  • Haramun Ne Mutane Su Kashe Wanda Ya Zagi Annabi - Malam Kabiru Gombe
    Sakataren Ƙungiyar Izala Ta Ƙasa kuma shahararren mai wa'azin nan, Malam Muhammad Kabiru Gombe ya ce, saɓawa Allah da faɗi Annabi Muhamm...
  • Ya Kamata Kowane Ma'aikaci Ya Auri Bazawara Daya - Shugabar Zaurawan Nigeria
    YA KAMATA KOWANE MA'AIKACI YA AURI BAZAWARA DAYA .....Inji shugabar Zaurawan Nigeria Shugabar kungiyar mata ZAURAWA ta Nigeria Hajiya ...

Facebook Page

ads 1

Ads 2

Powered by Blogger.
  • Home

Subscribe to 1Arewa TV



Like Our Facebook Page

Report Abuse

Search This Blog

Blog Archive

  • ►  2024 (11)
    • ►  August (5)
    • ►  June (2)
    • ►  April (4)
  • ►  2022 (2)
    • ►  March (2)
  • ►  2020 (28)
    • ►  August (9)
    • ►  July (14)
    • ►  May (2)
    • ►  March (1)
    • ►  February (2)
  • ►  2019 (4)
    • ►  November (3)
    • ►  October (1)
  • ►  2018 (762)
    • ►  September (2)
    • ►  August (2)
    • ►  June (70)
    • ►  May (98)
    • ►  April (48)
    • ►  March (408)
    • ►  February (127)
    • ►  January (7)
  • ►  2017 (1438)
    • ►  December (129)
    • ►  November (97)
    • ►  October (258)
    • ►  September (167)
    • ►  August (338)
    • ►  July (223)
    • ►  June (80)
    • ►  May (54)
    • ►  April (12)
    • ►  March (14)
    • ►  February (10)
    • ►  January (56)
  • ►  2016 (1350)
    • ►  December (82)
    • ►  November (108)
    • ►  October (197)
    • ►  September (199)
    • ►  August (118)
    • ►  July (43)
    • ►  June (74)
    • ►  May (70)
    • ►  April (89)
    • ►  March (128)
    • ►  February (149)
    • ►  January (93)
  • ▼  2015 (2312)
    • ▼  December (182)
      • Kungiyar Kare Hakkin Musulmi Ta Kasa Ta Mayarwa Da...
      • An Sace Wata Yar uwar Goodluck Jonathan
      • Kalaman Buhari Akan Sambo Dasuki
      • Kazamar Gida Part 13
      • Photos: Onazi A Wajen Siyan Kosai
      • Zainab Indomie Tana Raye Ba Ta Mutu Ba
      • Na Sha Jan Kunnen Sheik Zakzaky Kan Tare Hanya A Y...
      • Gobe Za A Yi Tattaunawar Kai Tsaye Da Shugaba Buhari
      • Photos: Anyi Hukunci Ma Wasu Mutane Guda Biyu Da S...
      • Waya Kashe Ta Part 2
      • Majalisar Dattawa Zata Gudanar Da Binciken Zariya
      • Kazamar Gida Part 12
      • Photos: An Sa Ranar Auren Yar Sanusi Lamido Sunusi...
      • Jam'iyyar APC Ta Jihar Kaduna Ta Dakatar Da Sanata...
      • Sanata Shehu Sani Ya Mayar Da Wasu Marayu 60 A Mat...
      • ILLAR Cin Mutuncin Dan'uwanka Musulmi
      • Kazamar Gida Part 11
      • Naushi Daya Na Yi Wa Abokina Ya Mutu
      • Dan Wasan Kwallo Kafa Nassarawa United Ya Rasu
      • Su Dawo Da Kudaden Da Suka Sata Ko Kuma Su Fuskanc...
      • Wa Ya Kashe Ta? Part 1
      • Photos..Nafisah Abdullahi A Dubai
      • Sojojin Najeriya Sun Kashe Yan Boko Haram 10
      • A Kalla Sama Da Mutane 20 Suka Rasa Rayukansu A Ha...
      • Za Mu Baiwa 'Yan Bangar JTF Damar Shiga Soja, - Ja...
      • Ban Je Kasar Dubai Domin Yi Wa Buhari Makarkashiya...
      • Graphic Photos : An Suka Wani Mutum Wuka A Egbeda
      • Tsohon Dogarin Osama Bin Laden ya rasu
      • Man Fetur Zai Wadaci Jama'ar Kasa Har Ya Zarce Buk...
      • Ya Kamata A Haramta Akidar Shi'a, Sakon Mazauna Ga...
      • Photos:An Bawa Aisha Buhari Wani Kyauta Hoton Buha...
      • Gwamna ElRufai Ba Zai Tada Masu Sayar Da Kilishi D...
      • Video: Epl Highlight Southampton 4 Arsenal 0
      • Batun Kudi Bai Taba Shiga Tsakanina Da Dasuki Ba, ...
      • Musulmai Da Kiristoci Sun Taya Juna Murnar Maulidi...
      • Photos:Anyi Bikin Yaron Burutai Yau
      • Video: Highlight Stoke City 2 Manchester United 0
      • Photos: Wanda Yafi Kowa Kiba A Duniya Ya Mutu
      • Photos:Zahra Buhari Da Takalma Dubu Dari Biyu
      • Hotunan Bikin Kirsimeti A Sansanin 'Yan Gudun Hiji...
      • Indan Baki Dawo Min Da Abinda Kika Dauka Ba Na Sakeki
      • Rikicin Yan Shi'a: Bincike Ne Ya Hana Ni Magana - ...
      • Mutane 8 sun rasu sakamakon gobara a matatar iskar...
      • Ladanin Masallaci Makkah Ya Rasu
      • Buhari Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa 85
      • Graphic Photos: Sama Da Mutane 100 Sun Koke Anambra
      • Photos: Aisha Buhari Ta Ziyarci Asibiti A Ranar Ch...
      • Photos: Buhari Da Jikokin Sa A Ranar Christmas
      • Yan Shi' Sun Zargi Gwamnatin Jihar Kaduna Da Rushe...
      • Addu'ar Mu A Kullum
      • Photos: Happy Birthday Ibrahim Birniwa
      • [Photos] Yan Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Jihar Kano
      • Ku Daina Sukar Gwamnatin Buhari, Sakon Jam'iyyar P...
      • Buhari Ya Warewa Tsoffin Shugabannin Kasa Naira Bi...
      • Ana Ci Gaba Da Karancin Man Fetur
      • An Haramta Shagulgulan Kiristimeti A Kasashen Brun...
      • Majalisar Matasan Musulman Nijeriya Ta Lashi Takob...
      • Babu Shugabancin APC A Kaduna, Saidai 'Yan Amshin ...
      • Shugaba Buhari Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Shekara...
      • Rashin Taka Rawar Gwamnatin APC Zai Iya Sanya Wa P...
      • Da Akwai Lauje Cikin Nadi, Akan Batun Tsare Zakzak...
      • Buhari ya bayar da hakuri kan matsalar fetur
      • Jonathan Ne Silar Wahalar Man Fetur Da Ake Ciki A ...
      • Video:Download Highlight Arsenal 2 Manchester City 1
      • Dasuki Na Ci Gaba Da Zama A Gidan Kurkukun Kuje
      • Photos: Likitoci Sunyi Nasarar Raba wasu Yara Da A...
      • Kwamitin Bincike Ya Wanke Wani Da Aka Sanya Hotons...
      • Gwamna El-Rufa'i Masoyin Mutane Ne'
      • ATM din Nigeria zai daina aiki a kasar waje
      • Graphic Photos: Sojojin Nijeriya Sun Kashe Amir Di...
      • Bisine Daruruwan 'Yan Shi'a A Wagegen Rami Bayan K...
      • Yadda dan kasuwa ya hallaka matashi wajen cire kod...
      • FIFA ta dakatar da Blatter da Platini na tsawon sh...
      • An Sace Kanwar Gwamnan Bayelsa
      • Video: Download Highlight Real Madrid 10-2 Rayo Va...
      • Sheikh Dahiru Usman Bauchi Yayi Magana Akan Rikici...
      • Maganin Ciwon Sanyi
      • Yan mata Ya Labarin Kwalliya A Lokacin Hunturu
      • Yan Sanda Sun Cafke Masu Kera Makamai A Jigawa
      • yan sanda sun saki mabiya shi`a
      • Photos:Hotuna Daga Wajen Bikin Murna Ranar Haihuwa...
      • Photos: Yan Shi'a Su Na Zanga-Zanga A Jihar Gombe
      • Rundunar 'Yan Sanda Ta Kori Gurbatattun Jami'anta ...
      • Photos: Ambode, El-Rufai Da Sarkin Kano Awajen Wan...
      • El Zakzaky Ba Ya Hannunmu, Inji Buratai
      • Photos: Fasto Mbaka Ya Ziyarci Buhari
      • Graphic Photos: Mutane Biyar Sun Rasa Rayukansu Ya...
      • Photos: Hotunan Yaran Sarkin Kano Akan Doki
      • An Karbi Beli Dasuki Da Saura Mutane 4
      • Tafsir: Tattalin Domin Ranar Mutuwa By Sheikh Ahma...
      • Kyautar Bikin Christmas: Halal Ko Haram
      • Photos: Aisha Buhari Ta Shiryawa Mijinta Bikin Mur...
      • An Cafke Wasu Masu Satar Mai
      • An Yi Yunkurin Juyin Mulki A Nijar
      • Diezani Tana Raye Bata Mutu Ba
      • Photos: Sabin Hotuna Zahra da Halima Buhari
      • Chelsea ta kori Jose Mourinho
      • Abin Da Shugaban Iran Ya Fadawa Buhari Akan Rikici...
      • Mutane 35 Sun Rasa Ransu A Wani Hadarin Kwale-kwal...
      • Sarkin Kano Yayi Magana Akan Rikicin Yan Shi'a
    • ►  November (308)
    • ►  October (389)
    • ►  September (198)
    • ►  August (182)
    • ►  July (211)
    • ►  June (216)
    • ►  May (239)
    • ►  April (187)
    • ►  March (116)
    • ►  February (54)
    • ►  January (30)
  • ►  2014 (7)
    • ►  December (6)
    • ►  January (1)

Labels

  • Al'ajabi
  • Arewa
  • Bollywood
  • Daga Jama'a
  • English News
  • Fadakarwa
  • Fadakarwa Labarai
  • family
  • Family related
  • Fasaha
  • Gida Nijeriya
  • Girke-girke
  • Hausa
  • Hausa Article
  • Hausa Film
  • Hausa HipHop
  • Hausa HipHop Music
  • Hausa Musi
  • Hausa Music
  • Hausa Novels
  • HipHop Music
  • Hollywood
  • Islamic
  • Kan
  • Kannywood
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai :
  • Labarai kannywood
  • Labari
  • Labari Al'ajabi
  • Labari. Gida Nijeriya
  • Labarin Siyasa
  • Labarin Wasanni
  • Labarun Duniya
  • Mu Sha Dariya
  • News
  • Nollywood
  • Photos
  • Rariya
  • Rayuwar Duniya
  • Sadarwa
  • Siyasa
  • Slider
  • Sports
  • Tafsir
  • Tarihi
  • Video

Main

  • Home

Populars

  • See How Every Premier League Teams Home Kit For 2024/25 Ranked
      The Premier League is not just a showcase of world-class football talent; it's also a platform for some of the most iconic and stylish...
  • Abubuwa Goma Da Sadiya Haruna Ta Fada Akan Gfresh A Hiran Da Tayi Hadiza...
  • Zuwa Da Budurwa Yawon Duniya ( Kalli Kaci Dariya)
  • Rikicin Tsakanin Hadiza Gabon Da Zaharadeen Sani ( Bayanai Da Rahoto) S...
  • The Missing seven-year-old boy found dead in Kano
    Seven-year-old Khalifa Saminu Saleh was tragically found deceased six days after he was reported missing in the Kuruma community...
  • Sadiya Gombe Ft Al'ameen Bauchi (Ra'ayin Ki Ne Nawa) Sabuwar Waka
  • Fatima Mai Zogale - Sabuwar Waka Rarara Ya Jawo Cece-Kuce
    Sabuwar Waka Rarara Me Taken Fatima Mai Zogale ya jawo Cece-Kuce a industry Kannywood Kalli wanna bidiyo domin Cikakken Bayanai Ga Bidiyon  ...
  • Zanga-zanga A Bauchi-Gwamnatin Ta Saka Dokar Hana Fita Da Zirga-Zirga Ac...
  • Bullying in Elite Educational Institutions: A Case Study from Abuja
    In the heart of Nigeria’s capital, Abuja, lies a stark contrast between the city’s opulent infrastructure and the troubling issu...
  • Barrister Aysha Ahmad - Kira Da Babban Muryan ( Akan Fyade Da Cin Zarafi...

Navigation

social Media

Categories

Al'ajabi Arewa Bollywood Daga Jama'a English News Fadakarwa Fadakarwa Labarai family Family related Fasaha Gida Nijeriya Girke-girke Hausa Hausa Article Hausa Film Hausa HipHop Hausa HipHop Music Hausa Musi Hausa Music Hausa Novels HipHop Music Hollywood Islamic Kan Kannywood Kiwon Lafiya Labarai Labarai : Labarai kannywood Labari Labari Al'ajabi Labari. Gida Nijeriya Labarin Siyasa Labarin Wasanni Labarun Duniya Mu Sha Dariya News Nollywood Photos Rariya Rayuwar Duniya Sadarwa Siyasa Slider Sports Tafsir Tarihi Video
Copyright 2012 1Arewa || Hausa Entertainment and News Blog - All Rights Reserved
Design by Abdul Mk
Powered by Blogger